Type Here to Get Search Results !

Yadda saurayi mai shekara 23 ya yi wa yarinya mai shekara 3 fyade, duba abin da ya faru

Rundunar yansandan jihar Osun ta kama wani saurayi mai suna Badmus Quadri mai shekara 23 bayan ya yi wa diyar makwabcinsa mai shekara 3 fyade.

An kama Badmus ranar Alhamis 11 ga watan Yuni, bayan makwabciyarsa ta shigar da kara a kansa a ofishin yansanda da ke Owode Egbado.

Mahaifiyar yarinyar ta shaida wa yansanda cewa ta gan jini yana fitowa daga al'aurar diyarta mai shekara 3, bayan ta tambayeta ko me ya faru da ita sai ta ce Badmus ne ya kai ta dakinsa ya yi lalata da ita.

Sakamakon haka, DPO na ofishin yansanda na Owode Egbado, SP Olabisi Elebutte ta jagoranci masu bincike suka kama Badmus nan take.

Kakakin hukumar yansanda na jihar Osun DSP Abimbola Oyeleye ya tabbatar da faruwarv lamarin., yayin da aka garzaya zuwa Asibitin Idiroko da yarinyar domin samun kulawan Likita.

Haka zalika bayanai sun ce Kwamishinan yansandan jihar Osun ya bayar da umarnin gudanar da cikakken bincike kan lamarin tare da ganin cewa an hukunta mai laifin.

Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp
https://chat.whatsapp.com/CSYKJgAmLEF4s1dle0Ug6J

Domin aiko labari, shawara ko tuntubarmu
LATSA NAN

SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA

Facebook.com/isyakulabari


Post a Comment

0 Comments
* Please Don't Spam Here. All the Comments are Reviewed by Admin.

Top Post Ad

Below Post Ad

Shiga group dinmu na WhatsApp domin samun labaran mu kai tsaye LATSA NAN
Domin zama Wakilin mu a garin ku LATSA NAN
Domin aiko Sako/Labari/Korafi LATSA NAN
Domin samun labaran mu a Facebook LATSA NAN
Domin samun labaranmu a Twitter LATSA NAN