Wani uba a ya karbo maganin Bindiga dan baiwa danshi kariya daga Harin
Fulani makiyaya, an yi rahin saa maganin bai yi ba inda ya durkawa dan
nasa harsashi.Saidai abin farin ciki shine dan nasa bai mutu ba,
Ya tsira. Daniel Qudus dake bayyana yana yanda lamatin ya faru a hannun
‘yansandan jihar Oyo ya bayyana cewa dansa yana dawowa gida daga gona
da dare kuma akwai matsalar Fulani Makiyaya dake kai musu hari, yace
wannan ne yasa dole ya dukufa nemarwa dansa maganin bindiga.
Ya kara da
cewa ya je wajan wani me bada maganin gargajiya inda ya samo maganin
kuma yace masa idan yazo gida ya gwada. Yace wajan gwajine sai aka harbi
danshi.Shima dai wanda ya bayar da maganin,
Akiyemi ya bayyana cewa shi
ba maganin bindiga ya baiwa Daniel ba, maganin habakar kasuwanci ya
bashi. Yace kawai yana zaune sai ga Daniel da danshi jinajina wai ya
cire masa harsashin dake jikinshi. Yace ko kulashi bai yi ba tunda shi
ba likita bane.
Kwamishinan ‘yansandan jihar, Mr. Nwachukwu Enwonwu ya bayyana cewa duka wanda ake zargin za’a gurfanar dasu gaban kuliya.
Hutudole
DAGA ISYAKU.COM
https://chat.whatsapp.com/CSYKJgAmLEF4s1dle0Ug6J
Domin aiko labari, shawara ko tuntubarmu
LATSA NAN
SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA
Facebook.com/isyakulabari