Da Duminsa: Kotu ta ce hukumar ‘yansanda su biya ‘yan Shi’a diyyar Miliyan 15 saboda kashe musu mutane 3

Rahotanni daga babban bornin tarayya, Abuja na cewa babbar kotun gwamnatin tarayya dake Abuja ta ci tarar hukukar ‘yansanda Naira Miliyan 15 kan kisan ‘yan Shi’a 3 inda ta bukaci a biya ‘yan shi’ar kudin a matsayin diyya.

Mai shari’a Taiwo Taiwo ne ya yanke wannan hukunci a yau, Litinin inda kuma ya bukaci babban Asibitin Abuja da ya baiwa ‘yan Shi’ar gawar mamatan.

Mai Shari’a Taiwo Taiwo ya bayyana cewa a biya kowane daga cikin masu karar su 3 diyyar Miliyan 5 saboda kashe musu ‘yan uwa.

Kamfanin dillancin Labaran Najeriya,NAN ya ruwaito cewa saidai Mai shari’a Taiwo ya ki amincewa da bukatar ‘yan Shi’ar kan tursasa Hukumar ‘yansandan ta basu hakuri ta hanyar bugawa a jarida saboda kisan.

Wanda aka kashe din sune, Sulaiman Shehu, Mahdi Musa, Bilyaminu Abubakar Faska, da Askari Hassan. Saidai har aka yi Shari’ar aka gama hukumar ‘yansadan Najeriya bata aike da wakili ba ko kuma lauya.

Hutudole


Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp
https://chat.whatsapp.com/CSYKJgAmLEF4s1dle0Ug6J

Domin aiko labari, shawara ko tuntubarmu
LATSA NAN

SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA

Facebook.com/isyakulabari



Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN