Type Here to Get Search Results !

Da Duminsa: Kotu ta ce hukumar ‘yansanda su biya ‘yan Shi’a diyyar Miliyan 15 saboda kashe musu mutane 3

Rahotanni daga babban bornin tarayya, Abuja na cewa babbar kotun gwamnatin tarayya dake Abuja ta ci tarar hukukar ‘yansanda Naira Miliyan 15 kan kisan ‘yan Shi’a 3 inda ta bukaci a biya ‘yan shi’ar kudin a matsayin diyya.

Mai shari’a Taiwo Taiwo ne ya yanke wannan hukunci a yau, Litinin inda kuma ya bukaci babban Asibitin Abuja da ya baiwa ‘yan Shi’ar gawar mamatan.

Mai Shari’a Taiwo Taiwo ya bayyana cewa a biya kowane daga cikin masu karar su 3 diyyar Miliyan 5 saboda kashe musu ‘yan uwa.

Kamfanin dillancin Labaran Najeriya,NAN ya ruwaito cewa saidai Mai shari’a Taiwo ya ki amincewa da bukatar ‘yan Shi’ar kan tursasa Hukumar ‘yansandan ta basu hakuri ta hanyar bugawa a jarida saboda kisan.

Wanda aka kashe din sune, Sulaiman Shehu, Mahdi Musa, Bilyaminu Abubakar Faska, da Askari Hassan. Saidai har aka yi Shari’ar aka gama hukumar ‘yansadan Najeriya bata aike da wakili ba ko kuma lauya.

Hutudole


Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp
https://chat.whatsapp.com/CSYKJgAmLEF4s1dle0Ug6J

Domin aiko labari, shawara ko tuntubarmu
LATSA NAN

SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA

Facebook.com/isyakulabari



Post a Comment

0 Comments
* Please Don't Spam Here. All the Comments are Reviewed by Admin.
Shiga group dinmu na WhatsApp domin samun labaran mu kai tsaye LATSA NAN
Domin zama Wakilin mu a garin ku LATSA NAN
Domin aiko Sako/Labari/Korafi LATSA NAN
Domin samun labaran mu a Facebook LATSA NAN
Domin samun labaranmu a Twitter LATSA NAN