'Yansanda sun halaka mai garkuwa da mutane, sun kwace tarin makamai

Rundunar yansandan jihat Rivers ta tabbatar da halaka kusurgumin mai satar mutane domin garkuwa da su  Samuel Naakpo, wanda ya dade yana addabar jama'ar da ke yamma maso gabacin hanyar Ogoni zuwa Uyo.

Kakakin hukumar yansandan jihar DSP Nnamdi Omoni ya sanar da haka, ya kuma ce an yi nassarar halaka Samuel ne bayan wani bayanin sirri da jami'an suka samu. Sakamakon haka suka je mabuyarsa amma ya arce da gudu, lamari da ya sa yansanda suka bindige shi a karamar hukumar Ogu-Bola.

An sami tarin makamai da albarussai da suka hada da bindigu kirar GMP No NN 07150, da  G-3.

DAGA ISYAKU.COM
Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp
https://chat.whatsapp.com/JC5tMMqXxKR6qWjM98ZwLA

Domin aiko labari, shawara ko tuntubarmu
LATSA NAN

SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA

Facebook.com/isyakulabari

Twitter.com/isyakulabari
Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN