Dalilai da yawa sun nuna mana cewa matan sauran kabilu sun
fi na Malam Bahaushe dadin zama, hakan ta sa a yau, za mu tattauna akan
wasu dalilai da ke sa matar Bahaushe rashin more dadin zaman aure kamar
haka:
1.Raini:
Akwai tsabar raini ga matar malam bahaushe, zaku zauna da
mace zhekara da shekaru amma rana daya matsala ta samu za ka ji
maganganu na raini ka ji suna cewa mazajensu kaddara ce ta sa suka aure
su.
Sai ka ji suna cewa ‘Idan ba kaddara ba, ba abunda zaisa na aure wane,
Ko kuma "Ai namiji ba dan goyo ba ne ba,
Sai ka ji suna cewa ‘Idan ba kaddara ba, ba abunda zaisa na aure wane,
Ko kuma "Ai namiji ba dan goyo ba ne ba,
Daman duk wacce ta dauki namiji uba za ta mutu marainiya da dai sauran kalamai irin wadannan
In muka yi wa wadannan kalamai fassara ta tsanaki, za mu fahimci abinda matar Bahaushe ke nufi da su.
Za mu gane manufarta ita ce kada mace ta sake ta baiwa mijinta yadda dari bisa dari, kada ta bashi soyayyarta duka. wanda kuma daga nanne matsalar auratayya ke farawa
Za mu gane manufarta ita ce kada mace ta sake ta baiwa mijinta yadda dari bisa dari, kada ta bashi soyayyarta duka. wanda kuma daga nanne matsalar auratayya ke farawa
Hakan tasa mazan hausawa da yawansu, suna zaune da matan sune bisa lalura kawai,
saboda abin haushi da kulawar da matan ke nuna musu wai da sunan kar su nunawa mazan soyayya da yarda wai don hakan zai iya cutar da su.
saboda abin haushi da kulawar da matan ke nuna musu wai da sunan kar su nunawa mazan soyayya da yarda wai don hakan zai iya cutar da su.
KUMA ABIN MAMAKI DA YAWAN MATAN HAUSAWA SUNA DA WANNAN RA’AYIN,
Sabanin sauran kabilu za ka same su basa raina mazajensu
2.Rashin yi wamiji hidima:
A nan ma za ka ga sauran matan kabilu suna yi wa mazajensu
wanki da guga da wanke takalmi da lura da kwalliyar maigida da gyara
masa ado, wasu har gona suke zuwa, daukar nauyin karatun 'ya’ya da
sauransu.
Amma matan bahaushe babu ruwansu, sai dai su ci su kwanta, babu ruwansu da mijinsu, balantana su yi masa wata hidima.
Hidimar kawai da za ta yi masa shi ne, ta dafa masa abinci, ko ta kai masa ruwan wanka.
BA WAI AN CE A ADDINANCE WAJIBI NE SAI TA YI HIDIMA KAMAR
BAIWA BA, A’A, AMMA TA FUSKAR MALLAKE MIJI DA NUNA MASA KAUNA SAI KIN YI
MASA HIDIMA DAI DAI DA ARZIKINSA,
MISALI GYARA MAMAKA SA KWALLIYA, GOGE MASA TAKALMI DA JAKA, DAURA MASA BELIT KO MADAURI WUYA,
GYARA MAKA SA FUSKA DA KILIFA,
GYARA MAKA SA HULA,
RIKE MASA JAKA, IN ZAKI IYA YI MASA WANKI MA TO BA LAIFI, AMMA BA TILAS.
Wadansu matan kabilun ma har yi wa mazansu sutura suke yi tare da yi musu kyaututtukan ba zata.
Duk wannan yana kara soyayya da shakuwa tsakanin ma’aurata
A nan ba ina nufin namiji ya kwanta kawai matarsa ta rika
yi masa hidima da bauta bane kamar yadda ake yi a wasu guraren kaga an
maida mata tamkar baiwa suyi casa suyi surfe suyi niqa,da shauran aikin
wahala hakan bai dace ba dan bautar da mata laifi ne a addininmu .
AMMA KODA MIJINKI MAI KUDI NE, TO YANA BUKATAR HIDIMA KODA DA KYAUTATAWA CE3
Rashin godiya:
Matar bahaushe tana da wata al’ada ta rashin godewa kokarin da mazajensu suke yi musu.
Ba su nuna godiyar a aikace ko kuma su furta da baka.
Ba su nuna godiyar a aikace ko kuma su furta da baka.
Akwai matan da suke cewa mazajensu mai suka taba yi musu tun da na zo hanunka
WANNAN KALMA CE MAI MUNI.
Daruruwan shekarun da suka gabata ANNABI S.A.W ya suffanta
mata masu irin wannan dabi’a,amma abin mamakin shi ne yadda kasan da
matan Hausawa Annabi S.A.W ya ke don bincike ya nuna sun fi sauran mata
fadarta.
Akwai nau’o’i na nunawa miji godiya, kuma
WALLAHI DUK SADDA KI KA NUNAWA MIJI GODIYA SAI YAJI YA KARA SONKI. KIN GA ASHE RIBARKI CE MA.
Amma abin haushi ‘yan kalmomi kadanda za ta furtawa mijinta
hade da murmushi da kyakkyawan kallo shike nan fa, kin farantawa
mijinki rai kin kara samun matsayi a zuciyarsa, ga kuma hidimar da ya yi
miki ga addu’ar da mala’iku za su yi miki
Sau tari, in Kaga matar Malam bahaushe tana yi wa mijinta godiya da fara’a to ta cuce shi ne ko kuma tana shirin cutarsa
4. Boye soyayya ga miji:
Ita ma wata dabi’a ce ta matan hausawa,rashin nunawa miji
soyayya sai dai baya-baya, dan wasu matan sun dauka nunawa miji soyayya
nasa miji ya raina ki.Wannan ma sai ya sa kaga ba a yi masa komai.
SU MATAN HAUSAWA ABINDA SUKA DAUKA NUNA SOYAYYA GA MIJI ITA CE KAWAI KWANCIYAR AURE,
bayan haka ba wata soyayya da suke nunawa mazajensu,Sau tari za ka ji matan wasu kabilun suna cewa “Wallahi da za su hada kishi da bahaushiya sai sun kwace mijin, ba malamai ba boka kawai tsantsar nunawa miji kulawa da soyayya da hidima.
5 .Watsar da kwalliya bayan aure da rashin iya tsara kwalliya:
Matar malam bahaushe da zarar ta yi aure bayan ta gama
cinye amarcinta hakanan za kaga ta watsar da dabi’arta ta kwalliya ta
koma daura zani iya kirji, kwaskwarima, bare ta fara tara 'ya’ya,
Subhanallah!
Hakanan suke har wajen tsarin sanya sutura, ba sa tsayawa su fahimci wace iriyar sutura ke burge mazajensu don rike irin wannan sutura a matsayin suturar da za su sanya a kebantaccen lokacinsu tare da mazajensu.
Hakanan suke har wajen tsarin sanya sutura, ba sa tsayawa su fahimci wace iriyar sutura ke burge mazajensu don rike irin wannan sutura a matsayin suturar da za su sanya a kebantaccen lokacinsu tare da mazajensu.
Wata sai kaga tana ta daura atamfa alhali siket da ‘yar riga ke burge mijinta
6:RASHIN IYA KISHI:
Matar bahaushe ba taiya kishi ba,
KISHI ANA YIN SA NE DON A MALLAKE MIJI TA HANYAR KYAUTATA MASA, AMMA ITA MATAR BAHAUSHE SAI DAI A BATAWA MIJI RAI.
Afuwa gareku matan Hausawa wannan bayani badan ya yi muku
zafi na yishi ba, a’a, illa kawai, don na tunatar da ku irin halayen
mafiya yawanku matanmu na Hausawa.
An yi muku nisa a fagen zamantakewa kamar yadda ku ka sani,
yau duniya ta ci gaba sosai a kowanne bangare, wannan kuwa ya hada har
da bangaren zamantakewa.
A saboda haka ne ma na ke yin kira a gareku da ku canja
Daga Alhaji Abdulyasar
DAGA ISYAKU.COM
Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp
https://chat.whatsapp.com/JC5tMMqXxKR6qWjM98ZwLA
Domin aiko labari, shawara ko tuntubarmu
LATSA NAN
SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA
Facebook.com/isyakulabari
Twitter.com/isyakulabari