COVID-19: An kama Limamai goma sha biyar a Kano sakamakon jagorantar Sallar Juma'a

Rundunar yansandan jihar Kano ta tabbatar da kama Limamai goma sha biyar bisa zargin saba dokar hana zirga zzirga da cinkoson jama'a saboda dakile cutar coronavirus a jihar.
 
Limaman da aka kama sun jagoranci Sallar Juma'a ne, wanda hakan ya saba wa doka da Gwamna Ganduje ya sanya saboda ,matsalar cutar Covid-19. Wadanda aka kama  Limaman Masallatan Juma'a ne a kananan hukumomin Birnin Kano watau Kano Municipal, Garko, Gwale, Karaye, da Tarauni.
 
Kakakin hukumar yansanda jihar Kano Abdullahi Haruna ya ce, jami'an hukumar Hisbah na jihar Kano ne suka kama Limaman, daga bisani suka mika su ga yansanda domin fuskantar tuhuma.
 
DAGA ISYAKU.COM
Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp
https://chat.whatsapp.com/JC5tMMqXxKR6qWjM98ZwLA

Domin aiko labari, shawara ko tuntubarmu
LATSA NAN

SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA

Facebook.com/isyakulabari

Twitter.com/isyakulabari
Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN