Rahotun Lagit Hausa
Rahotanni sun kawo cewa an tsaurara matakan tsaro a garin Awe na jahar Nasarawa, inda aka ajiye korarren sarkin Kano, Muhammadu Sanusi II tun bayan da Gwamna Abdullahi Umar Ganduje na jahar Kano ya tsige shi.
An gano jami’an rundunar sojin Najeriya, jami’an tsaro na yan sandan fari n kaya (DSS), yan sanda da kuma jami’an hukumar Civil Defence zube wadanda ke bayar da kariya ga tsigaggen sarkin, jaridar Daily Trust ta ruwaito.
Sai dai a wata hira da kwamishinan yan sandan jahar, Bola Longe, ya ce an zuba matakan tsaro ne a karamar hukumar Awe na jahar Nasarawa domin amfanin kowa.
"An zuba Karin jami’an tsaro ne a garin domin su kare mazauna yankin da baki a garin, ba wai don tsorata kowa ba.
DAGA ISYAKU.COMLatsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp
https://chat.whatsapp.com/JC5tMMqXxKR6qWjM98ZwLA
Duba kasuwanci da za ka sami ribar kaso 200 a rana daya kacal. LATSA NAN ka bincika
Domin aiko labari, shawara ko tuntubarmu
LATSA NAN