Shari'ar Kotun Koli: Malaman Musulunci sun yi wa Tambuwal wani muhimmin abu

Rahotun Legit Hausa

Malaman addinin Islama na jihar Sokoto sun hada sallah ta musamman don neman taimakon Allah a hukuncin da kotun koli zata yanke a kan nasarar Aminu Tambuwal da ake kalubalanta a jihar.

Idan zamu tuna, kotun kolin ta saka ranar 20 ga watan Janairu don jin hukuncin karshe na zaben 9 ga watan Maris na jihohin Kano, Sokoto, Benuwe, Filato da Adamawa.

Jaridar Daily Nigerian ta ruwaito cewa malaman sun hadu ne a babban masallacin idin jihar don yin addu'o'i. Malaman da suka jagoranci addu'o'in sun hada da Malam Tukur Rijiyar-Zaure, Malam Bala Marina, Malam Aliyu Danbaba da sauransu.

Wasu malaman da suka samu zantawa da manema labarai sun bayyana cewa matukar aka hana jama'ar jihar bukatarsu, suna tsoron zata yuwu zaman lafiya a jihar yayi kaura.

Kamar yadda suka tabbatar, zuwan Tambuwal a matsayin gwamnan jihar ya taimaka wajen fatattakar wasu kalubalen da jihar ke fuskanta wadanda suka hada da luwadi, ta'ammali da miyagun kwayoyi, daba da sauransu.

DAGA ISYAKU.COM
Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp
https://chat.whatsapp.com/DTV1WsH2ypv0WtRujXbA0F

Domin aiko labari, shawara ko tuntubarmu LATSA NAN

SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA

Facebook.com/isyakulabari

Twitter.com/isyakulabari
Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN