Legit Hausa
Wasu baragurbin jami’an hukumar kare haddura ta kasa, FRSC,
dake aiki a ofishinsu na Abudu jahar Edo sun kashe wani bawan Allah mai suna
Odion Samuel sa’annan suka binneshi cikin wani kabari mara zurfi, inji rahoton
jaridar Sahara Reporters.
Majiyar Legit.ng ta ruwaito sunayen jami’an da suka aikata
wannan aika aika kamar haka, Francis Igoh, Sunday Ogi, Samson Alolade da kuma
Joseph Onolade, kuma sun kashe Odion ne saboda ya hanasu karbar cin hanci da
rashawa daga hannun wani direba.
Wannan mummunan lamari ya auku ne a ranar 14 ga watan Oktoba
a kusa da tsaunin Okhuaihe dake kan babbar hanyar Bini zuwa Agbor, inda da fara
jami’an suka fara tsare motar tare da tuhumar direban motar da sacewa da kuma
yin garkuwa da Odion.
Sai dai daga bisani binciken Yansanda ya nuna cewa jami’an
FRSC ne suka kashe Odion, bayan sun sha dan karan tambaya daga wajen Yansanda
sai suka garzaya da Yansanda zuwa inda suka binne gawar mamacin.
Kaakakin Yansandan jahar Edo, DSP Chidi Nwabuzor ya tabbatar
da aukuwar lamarin, inda ya bayyana lamarin a matsayin laifin kisan kai da
gangan, sa’annan yace zasu gurfanar da mutanen biyu gaban kotu da zarar sun
kammala gudanar da bincike.
DAGA ISYAKU.COM Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp https://chat.whatsapp.com/Hp4xUtixUxh5d76Kw2TGpp