Legit Hausa
An tattaro cewa fashin ya afku ne da misalin karfe 2:30 na
rana inda suke ta harbi yayinda tawagarsu na mutum 10 suka shiga cikin bankin
na zamani. Jaridar premium Times ta ruwaito inda idanun shaida kecewa yan
fashin sun kwashe akalla mintuna 25 suna fashi bayan sun shigo garin cikin
motoci biyu ta hanyar Ikere.
Kakakin yan sandan jihar Ekiti, Mista Caleb Ikechukwu wanda
ya tabbatar da faruwar lamarin yace yan ta’addan sun fasa kofar tsaro na bankin
da nakiya sannan suka samu damar shiga ciki. Yace jami’an rundunar na kan bin
sahun yan ta’addan sannan yayi kira ga mazauna jihar da kada su sanya tsoro a
zukatansu.
A wani lamarin kuma, mun ji cewa rundunar 'yan sanda reshen
jihar Taraba ta ce ta kashe wani gawurtaccen dan fashi da makami da ta dade
tana nema ruwa a jallo.
A sanarwar da mai magana da yawun rundunar na jihar Taraba,
David Misal ya fitar, ya ce an yi nasarar kashe dan fashin ne bayan an sanar da
'yan sanda cewa wasu 'yan bindiga sun tare hanyar Jatau/Borno kuru-Ku a karamar
hukumar Bali na jihar Taraba suna yi wa mutane fashi.
A cewar sanarwar, 'yan sandan tare da hadin gwiwa 'yan
kungiyar sa kai sun garzaya inda lamarin ke faruwa kamar yadda Channels TV ta
ruwaito.
DAGA ISYAKU.COM
Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp
https://chat.whatsapp.com/D9SKfH2BjM4Deldar0KkFN