Legit Hausa
A Musulunce mace na fita daga gidan mijinta ne idan mijinta
ya furta da bakin shi cewa ya sake ta. Idan mace na so mijinta ya sake ta sai
ta bi wata hanya wacce addinin musulunci ya shar'anta, inda matar za ta je
gaban alkali ta nemi mijinta ya sake ta.
Zama da miji marar hakuri ga mace ba abu bane mai sauki,
hakan ya saka wata Balarabiya wacce ta kasa zuwa ta nemi kotu ta raba aurensu
ta bi wata hanya daban domin kawo karshen auren na su.
Matar ta shafe shekara uku tana zaune da mutumin wanda
kwata-kwata ba ta kaunar zama dashi, amma kuma mutumin yaki ya bata takardarta
ta saki. Hakan yasa matar ta yi kokarin yanke hukunci da kanta. Matar ta dauki
wayar mijinta a lokacin da yake yin bacci ta tura sakon saki har sau uku zuwa
cikin wayarta. Bayan wannan lamari ya faru, wani babban malamin addinin
musulunci ya bayyana cewa wannan saki ya yiwu.
Hakan ya sa mata da mijin suka tafi kotu domin neman ta
yanke hukunci. Bayan kotu ta saurari kowanne bangare, sai ta bukaci mijin ya
saki matarr, amma ina maimakon ya sake ta sai ya saka shari'ar ta yi tsawo da
yawa, an bayyana cewa mutumin yana yin hakan ne domin kaskantar da matar tashi
a idon duniya.
DAGA ISYAKU.COM
Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp
https://chat.whatsapp.com/D9SKfH2BjM4Deldar0KkFN
Tags:
LABARI