Legit Hausa
Gwamnatin jihar Zamfara ta kaddamar da wani bincike akan
sha’anin da ke tattare da al’amarin tsintar wasu fallayen Qur’ani a najasa a
makarantar Firamare a ranar Juma’a. An gano shafukan littafin mai tsarki ne a
makarantar Firamare na Shattima, Gusau, wanda yayi sanadiyar rufe makarantar
har sai baba-ya-gani da kuma dakatar da malaman makarantar bisa ga umurnin
gwamnan jihar, Alhaji Bello Matawalle.
Gwamnan wanda a yanzu haka ya halarci taron zuba jari na
Afrika a kasar Amurka, ya umurci hukumar makarantar Firamare da ya kafa
kwamitin bincike akan lamarin. A wani jawabi daga babban sakataren gwamnati
Alhaji Bala Maru, a Gusau a ranar Lahadi, 29 ga watan Satumba, gwamnatin ta
sanar da kafa kwamitin mutum 23, karkashin jagorancin Farfesa Jafaru Makau.
Sauna mambobin kwamitin sune manyan malaman addinin
Musulunci, wakilan hukumomin tsaro, ma’aikatu da abun ya shafa, cki harda
kungiyar lauyoyin Najeriya. Gwamnatin tayi alkawain bayar da kyautar naira
miliyan 2 ga duk mutumin da ya kawo bayanai masu amfani. Ya bukaci jama’a
musamman a Gusau da su kai rahoton duk wani motsi da basu aminta dashi ba a
kewayen su zuwa ga hukumar tsaro akan lokaci.
Gwamnatin jihar Zamfara
ta kaddamar da wani bincike akan sha’anin da ke tattare da al’amarin
tsintar wasu fallayen Qur’ani a najasa a makarantar Firamare a ranar
Juma’a.
An gano shafukan littafin mai tsarki ne a makarantar Firamare na
Shattima, Gusau, wanda yayi sanadiyar rufe makarantar har sai
baba-ya-gani da kuma dakatar da malaman makarantar bisa ga umurnin
gwamnan jihar, Alhaji Bello Matawalle.
Gwamnan wanda a yanzu haka ya halarci taron zuba jari na Afrika a kasar
Amurka, ya umurci hukumar makarantar Firamare da ya kafa kwamitin
bincike akan lamarin.
A wani jawabi daga babban sakataren gwamnati Alhaji Bala Maru, a Gusau a
ranar Lahadi, 29 ga watan Satumba, gwamnatin ta sanar da kafa kwamitin
mutum 23, karkashin jagorancin Farfesa Jafaru Makau.
Sauna mambobin kwamitin sune manyan malaman addinin Musulunci, wakilan
hukumomin tsaro, ma’aikatu da abun ya shafa, cki harda kungiyar lauyoyin
Najeriya.
Gwamnatin tayi alkawain bayar da kyautar naira miliyan 2 ga duk mutumin
da ya kawo bayanai masu amfani.
Ya bukaci jama’a musamman a Gusau da su kai rahoton duk wani motsi da
basu aminta dashi ba a kewayen su zuwa ga hukumar tsaro akan lokaci.
Read more: https://hausa.legit.ng/1262056-gwamnatin-zamfara-ta-sa-ayi-bincike-akan-batun-sanya-qurani-a-najasa-tayi-alkawarin-bayar-da-naira-miliyan-2-ga-duk-wanda-ya-kawo-bayanai.html
DAGA ISYAKU.COMLatsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp
https://chat.whatsapp.com/D9SKfH2BjM4Deldar0KkFN