Legit Hausa
Tsohon dan majalisa mai wakiltar mazabar Kaduna ta tsakiya a
majalisar dattawan Najeriya, Sanata Shehu Sani ya bayyana wata hanya daya
kwakkwara da yake ganin idan har aka bi ta za’a samu saukin matsalar tsaro da
ake fama dashi a yankin Arewacin Najeriya.
Legit.ng ta ruwaito Shehu ya bayyana haka ne a shafinsa na
kafar sadarwar zamani ta Facebook, inda yace da gwamnonin jahohin Arewa yake,
walau su karbi shawarsa ko su yi watsi dashi, amma akwai bukatar gwamnonin su
tattaro kwararru a harkar tsaro don ceto yankin.
“Idan har ana son kawo karshen matsalar tsaro a Arewacin
Najeriya, ya kamata gwamnonin Arewa su kafa wata kwamiti da zai kunshi mutane
kamarsu Janar Aliyu Gusau, Janar Magoro, Janar Agwai, Janar Buba Marwa, Kanal
Umar, Kanar Gwadabe.
“Da sauran tsofaffin sufetan Yansandan Najeriya da suka fito
daga yankin Arewa, da kuma tsofaffin jami’an tsaron farin kaya dana sirri yan
asalin yankin Arewa domin su zauna tare su tattauna matsalar tare da samar da
hanya daya wanda za’a bi, su fidda rahoto.
“Kuma gwamnonin su tabbata sun aiwatar da rahoton wannan
kwamiti domin taimaka ma kokarin da gwamnatin tarayya ke yi don magance
matsalar kashe kashe da garkuwa da mutane a yankin.
” Inji shi. A wani labarin kuma, a sakamakon tabarbarewar
tsaro a kan babbar hanyar Kaduna zuwa Abuja, musamman a cikin makonnan inda yan
bindiga suka ci karensu babu babbaka, babban sufetan Yansandan Najeriya ta sake
shirin yaki da miyagun.
A yau ne babban sufetan Yansandan Najeriya, Mohammed Adamu
ya aika da tawagar yansanda ta musamman dake kai agajin gaggawa, IRT, zuwa
hanyar Kaduna-Abuja a karkashin jagorancin jarumin Dansanda, DCP Abba Kyari don
tabbatar da tsaro a kan hanyar.
DAGA ISYAKU.COM
Latsa Shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp
https://chat.whatsapp.com/D9SKfH2BjM4Deldar0KkFN