Legit Hausa
Ibrahim Tanko Muhammed, sabon mukaddashin shugaban alkalan
Najeriya (CJN) a ranar Asabar, 26 ga watan Janairu ya rantsar da mambobin
kwamitin sauraron kararrakin zabe su 250, gidan talbijin din Channels TV ta
ruwaito.
A lokacin bikin kaddamarwar da ya gudana a Abuja a ranar
Asabar, Muhammed ya bukaci mambobin kwamitin sauraron kararrakin zaben da su
gudanar da ayyukansu cikin mutunci da tsoron Allah a zukatansu. Da farko,
Legit.ng ta rahoto sabbin bayanai da suka billo kan dalilin da yasa gwamnatin
tarayya ba ta jira kotu ta bayar da umurni akan tsige babban alkalin-alkalan
Najeriya Walter Onnoghen ba a Abuja a ranar Asabar, 26 ga watan Janairu.
An sanya ran cewa Justice Onnoghen zai kaddamar da
kwamitocin alkalai 250 da za su jagoranci gudanarwar zabe mai zuwa. Majiyar
tace: “Adadin mambobin da za su zauna a kwamitocin zabe su 250 ne. Kwamitocin
sun hada da na sauraron kararrakin zaben yan majalisar dokoki, kotun sauraron
kararrakin zaben gwamna, da kuma na sauraron kararrakin zaben yan majalisar
dokoki na jiha.
“Cire shi da aka yi cikin gaggawa don kokarin dakatar da
taron ne ko kuma yunkurin cire sunayen wasu alkalai daga jerin sunayen. Hakan
ce za ta kasance."
DAGA ISYAKU.COM
Ku biyo mu a Facebook facebook.com/isyakunews
Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> https://chat.whatsapp.com/KIHbQShlAs2GexpIYyxleG
Domin GYARA wayarka ko FLASHING ka zo SENIORA TECH shago mai lamba 50 hawa na sama, TAUSHI PLAZA, Ahmadu Bello Way Birnin kebbi