Kiristoci Ne Suka Taimake Ni Lokacin Da Musulmi Suka Juya Mini Baya - Buhari

Legit Hausa


Shugaba Muhammadu Buhari ya nuna bacin ransa a kan halayen wasu 'yan Najeriya da ke amfani da kabilanci ko addini domin aikata zalunci da aikata rashawa inda ya ce yaudara ce da shirme. A jawabin da ya yi a wurin taron cin abinci na musamman inda ya gayyaci tsaffin abokan aikinsa yayin da ya ke mulkin soja (tsakanin 1984-1985) da aka gudanar a ranar Lahadi a fadar Aso Rock, shugaban kasar ya ce rashawa ce ke sanya wasu boyewa cikin rigar addini da kabilanci.

Domin kafa hujja a kan abinda ya fadi, shugaban kasar ya bayar da labarin gwagwarmayar da sha a kotun zabe a shekarun 2003, 2007 da 2011 inda 'yan uwansa musulmi 'yan arewa ne suka kayar da shi yayin da Kiristoci daga kudu ke kare shi. Ga wani sashi cikin jawabinsa: "Wasu dalilai sun sanya ni magana a kan wani da nake matukar mutuntawa a Najeriya.

A 2003 da na fara, ana fara shigar da karar zaben shugaban kasa ne daga kotun daukaka kara. A lokacin shugaban kotun ajin mu daya da shi a makarantar sakandire, ni da shi da Shehu Musa Yaradua duk ajin mu daya. Lauya na a wannan lokacin, Mike Ahamba kirista ne kuma Ibo. Zuwa na kotu ranar farko, Ahamba ya ce min yana bukatar jerin sunayen wadanda su kayi rajistan zabe a wasu yankuna domin ya nuna cewa kuri'un da aka samu a wuraren na bogi ne.

Ya bukaci su rubuta bukatarsa kuma su rattaba hannu, kuma su kayi hakan. "A yayin da suka zo yanke hukunci, sai suka ki ambaton zancen. A cikin jerin alkalan wani Kirista kuma dan kabilar Ibo ne ya daga hannunsa ya tunatar da su abinda lauya na nema. Shin mun nemi a bamu rajistan wadanda su kayi zabe a wadannan yankunan? Idan ba muyi ba kuma menene dalili? Nan suka yi masa taron dangi suka ce ya yi shiri. Hakan yasa ya rubuta hukuncinsa daban da nasu.

A yau shine jakadar Najeriya a Amurka. "Na shigar da kara a kotun koli. Wanene babban alkalin kotun? Musulmi ne Fulani daga Zaria. Bayan watanni 27, mun sake komawa kotun. Ahamba ya yi bayani na sa'o'i 2 da mintuna 45 amma suka ce masa za su tafi hutu a goben ranar. Sunyi hutu na watanni 3 kuma da suka dawo hutun su kayi watsi da shar'ar namu cikin mintuna 45.

"A 2007, abinda ya sake faruwa kenan. Wanenen Alkalin Alkalai? Musulmi ne dan Arewa kuma bayan watanni 18 su kayi watsi da shar'ar. "A karo na 3 a 2011, Alkalin alkalai shima musulmi ne, Fulani daga jihar Jigawa. Bayan watanni 8 ya yi watsi da shar'iar. Saboda haka batun amfani da kabilanci da addini a Najeriya wurin cimma wasu manufofi rashawa ne tsantsagwaronta. Duk ida muka samu kanmu, muji tsoron Allah mu tsare imanin mu."
 

DAGA ISYAKU.COM

Ku biyo mu a Facebook facebook.com/isyakunews

 Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> https://chat.whatsapp.com/KIHbQShlAs2GexpIYyxleG

Domin GYARA wayarka ko FLASHING ka zo SENIORA TECH shago mai lamba 50 hawa na sama, TAUSHI PLAZA, Ahmadu Bello Way Birnin kebbi
Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN