Jihar Kebbi tana kan shirin tarbon babban bako na siyasa shugaba Muhammadu Buhari da tawagarsa za ta sauka a garin Birnin kebbi a ci gaba da zagayen yakin neman zabe na shugaban kasa da yake yi. Ana kyautata zaton shugaba Buhari zai iso garin Birnin kebbi da karfe 3:00 na rana a Filin wasa na Haliru Abdu.
Bisa wannan dalili ne Gwamna Atiku Bagudu na jihar Kebbi tare da rakiyar tsohon Gwamnan jihar Kebbi Sa'idu Dakingari, da Mataimakinsa K. Aliyu da sauran hadiman Gwamna Bagudu, suka kai ziyarar bazata na gani da ido yadda aikin hada wajen taron ke tafiya. Gwamna Bagudu ya isa filin wasa na Haliru Abdu da misalin karfe 5;17 na yamma.
Ga dukkan lamu a cikin darae ne za a hada rumfa da za'a yi taron kasancewa har zuwa wannan lokaci ba'a fara hada rumfarba, amma ana gudanar da aiki ba kama hannun yaro.
An ga jami'an tsaro na yansandan ganowa da kwance bamabamai suna gudanar da aiki a wannan fili.
Bayan kimanin minti 15 da zagayen wajen aikin a filin wasa na Haliru Abdu, Gwamna Bagudu ya fice daga filin wasar tare da 'yan rakiyarsa da suka shiga wata motar bas mai kalar ruwan madara gaba dayansu.
Gwaamna Bagudu yana daya daga cikin Gwamnonin Arewa da ke dadi da shugaba Buhari, wanda bayanai suka nuna ya samo asali bisa dagewa da jihar Kebbi ta yi wajen noman shinkafa da ya jawo ma Najeriya daraja a fuskan kasashen Duniya, kuma haka ya faranta ran shugaba Buhari.
DAGA ISYAKU.COM
Ku biyo mu a Facebook facebook.com/isyakunews
Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> https://chat.whatsapp.com/KIHbQShlAs2GexpIYyxleG
Domin GYARA wayarka ko FLASHING ka zo SENIORA TECH shago mai lamba 50 hawa na sama, TAUSHI PLAZA, Ahmadu Bello Way Birnin kebbi
Bisa wannan dalili ne Gwamna Atiku Bagudu na jihar Kebbi tare da rakiyar tsohon Gwamnan jihar Kebbi Sa'idu Dakingari, da Mataimakinsa K. Aliyu da sauran hadiman Gwamna Bagudu, suka kai ziyarar bazata na gani da ido yadda aikin hada wajen taron ke tafiya. Gwamna Bagudu ya isa filin wasa na Haliru Abdu da misalin karfe 5;17 na yamma.
Ga dukkan lamu a cikin darae ne za a hada rumfa da za'a yi taron kasancewa har zuwa wannan lokaci ba'a fara hada rumfarba, amma ana gudanar da aiki ba kama hannun yaro.
An ga jami'an tsaro na yansandan ganowa da kwance bamabamai suna gudanar da aiki a wannan fili.
Gwaamna Bagudu yana daya daga cikin Gwamnonin Arewa da ke dadi da shugaba Buhari, wanda bayanai suka nuna ya samo asali bisa dagewa da jihar Kebbi ta yi wajen noman shinkafa da ya jawo ma Najeriya daraja a fuskan kasashen Duniya, kuma haka ya faranta ran shugaba Buhari.
DAGA ISYAKU.COM
Ku biyo mu a Facebook facebook.com/isyakunews
Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> https://chat.whatsapp.com/KIHbQShlAs2GexpIYyxleG
Domin GYARA wayarka ko FLASHING ka zo SENIORA TECH shago mai lamba 50 hawa na sama, TAUSHI PLAZA, Ahmadu Bello Way Birnin kebbi