Legit Hausa
Ana gudanar da wannan biki ne a duk
fadin duniya a ranar 11 ga watan Nuwamba don tunawa da ranar da yakin tunawa
karshen yakin Duniya na daya, tare da Sojojin da suka mutu, sai dai Najeriya ta
canza nata ranar zuwa 15 ga watan Janairu, ranar da yakin basasa yak are, 15 ga
watan Janairu na 1970.
Majiyar Legit.ng ta ruwaito shugaban
kasa Muhammadu Buhari da mataimakinsa Osinbajo sun samu halartar bikin da aka
gudanar a babban birnin tarayya Abuja, inda aka hangesu suna jingine fulawa a
matsayin wata hanyar girmamawa ga mamatan.
Haka zalika, shugaban majalisar
dattawan Najeriya, Sanata Bukola Saraki, Kaakakin majalisar wakilai Yakubu
Dogara, Alkalin Alkalai, Ministan Abuja, da Ministan kudi duk ni sawun shugaba
Buhari wajen jingine fulawar.
Sauran sun hada da shugaban
hafsoshin rundunonin Sojin Najeriya, Janar Abayomi Olanisakin, babban hafsan
Sojan kasa, Laftanar Janar Tukuru Buratai, babban hafsan Sojan sama, Sadiqque
Abubakar, babban hafsan sojan ruwa da tsohon babban sufetan Yansanda, Ibrahim
Idris da kuma ministan tsaro Mansur Dan Ali.
Bugu da kari shugaba Buhari ya saki
wasu fararen tantanbaru, wani alama dake nuni da zaman layi, sa’annan yayi
gabatar da jawabi ga yan uwan mamatan da suka samu halartar bikin, sa’annan ya
bi sauran manyan bakin da suka halarta da gaisuwa. Sai dai wasu daga cikin
iyalan mamatan da suka halarci bikin sun koka da yadda gwamnatin Najeriya ke
nuna musu halin ko in kula game da mawuyacin halin da suka afka tun bayan
mutuwar mazajensu ko iyayensu Sojoji.
DAGA ISYAKU.COM
Ku biyo mu a Facebook facebook.com/isyakunews
Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> https://chat.whatsapp.com/KIHbQShlAs2GexpIYyxleG
Domin GYARA wayarka ko FLASHING ka zo SENIORA TECH shago mai lamba 50 hawa na sama, TAUSHI PLAZA, Ahmadu Bello Way Birnin kebbi