Type Here to Get Search Results !

Main event

Karin Albashi: Gwamnati bata shirya biya ba - NLC


Shugaban kungiyar kwadago ta kasa, Ayuba Wabba, ya zargi Gwamnatin tarayya da ministan kwadago, Sanata Chris Ngige da tsayar da karin karancin albashin, yace ma'aikata bazasu cigaba da hakuri ba. Ansan cewa zuwa 21 ga watan Augusta na zasu kammala aikin da kwamitin karin karancin albashin, amma sai Ministan Kwadago yace Gwamnatin tarayya bata shirya ba.

"Hakan na nuna cewa basu shirya tabbatar da karin karancin albashin ba a ranar 4 da 5 ga watan satumba, duk da mu dai mun kammala shirye shiryen mu " inji Wabba. " Za'a iya tunawa cewa, an nada kwamitin ne tun a watan Nuwamba 2017 amma basu fara aiki ba sai a watan Maris, akan dalilin da su kadai suka sani."

Kamar yanda tsarin aikin ya nuna, yakamata mu kammala ne zuwa 21 ga watan Augusta, amma sai ya fada a ranar hutu Hakan yasa aka maida zuwa 4 da 5 ga watan Satumba. A wannan taron ne yakamata mu kammala dukkan rahoto, sannan mu kawo karshen aikin.

 Amma kafin mu kammala sai ministan kwadago, a matsayin wakilin Gwamnatin tarayya ya tashi yace suna da bukata tataunawa kafin su tsayar da karancin albashin. Inji Wabba
 

Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> whatsapp://chat?code=41x2TuRqdVQ9PrcrucqpTu Shiga cikakken shafin mu kai tsaye www.isyaku.com Tuntube mu ta SMS ko TEXT kawai zuwa 08087645001 ba mu amsa kira

Hausa.naij.ng

Post a Comment

0 Comments
* Please Don't Spam Here. All the Comments are Reviewed by Admin.

Top Post Ad

Below Post Ad

Shiga group dinmu na WhatsApp domin samun labaran mu kai tsaye LATSA NAN
Domin zama Wakilin mu a garin ku LATSA NAN
Domin aiko Sako/Labari/Korafi LATSA NAN
Domin samun labaran mu a Facebook LATSA NAN
Domin samun labaranmu a Twitter LATSA NAN

Hollywood Movies