Kamar yadda kamfanin
dillancin labarai na Najeriya ya ruwaito, wani babban ma'aikacin
gwamnatin jihar Zamfara ya bayyana cewa, sauran ƙiris a kammala aikin
titin garin Kauran Namoda, Birnin Magaji da kuma Dauran dake jihar
Zamfara. Read more: https://hausa.naija.ng/1184435-sauran-kiris-a-kammala-babbar-hanyar-kauran-namoda-zuwa-birnin-magaji-a-jihar-zamfara.html#118443Kamar yadda kamfanin dillancin labarai na Najeriya ya
ruwaito, wani babban ma'aikacin gwamnatin jihar Zamfara ya bayyana cewa, sauran
ƙiris a kammala aikin titin garin Kauran Namoda, Birnin Magaji da kuma Dauran
dake jihar Zamfara.
Kamar yadda kamfanin dillancin labarai na Najeriya ya
ruwaito, wani babban ma'aikacin gwamnatin jihar Zamfara ya bayyana cewa, sauran
ƙiris a kammala aikin titin garin Kauran Namoda, Birnin Magaji da kuma Dauran
dake jihar Zamfara.
Kwamishinan na ma'aikatar kasafi da tsare-tsaren tattalin
arzikin na jihar, Alhaji Ibrahim Birnin Magaji, shine ya bayyana hakan yayin
wata ganawa da manema labarai da gudana cikin Kanon Dabo a ranar Juma'ar da ta
gabata. Yake cewa, gwamnatin jihar karkashin jagorancin gwamna Abdulaziz
Abubakar Yari, ta fito ƙwanta da kwarkwata tare da jajircewa wajen gudanar da
wannan babban aiki sakamakon bukatar al'ummar yakunan da suka shafe shekaru
aru-aru su na kiran gwamnatocin da suka shude.
Bayan tsawon shekaru kimanin 40 da suka shude, gwamna Yari
ya bayyana fifikonsa a zahiri tare hangen muhimmancin wannan katafaren aiki da
zai matukar bunkasa tattalin arziki a jihar. Kwamshinan yake cewa, an kammala
kaso 98 cikin 100 na wannan babban aiki da a sanadiyar haka ne gwamnatin jihar
tuni ta aika da sakon ta ga shugaban kasa Muhammadu Buhari domin ya kaddamar da
aikin da zarar ya kammalu baki daya. Ya ci gaba da cewa, wannan babbar hanya za
ta inganta tare da taka rawar gani wajen bunkasar tattalin arziki ga al'ummar
jihar da kuma makociyar jiha ta Katsina.
Kazalika Birnin Magaji ya kara da cewa, gwamnatin jihar ta
malalar da dukiya ta kimanin Naira miliyan 700 wajen gudanar da gyara a babban
asibitin Birnin Magaji tare da samar da tsaftataccen ruwa sha ga kauyukan dake
makotaka da yankin.
Kamfanin dillancin labarai na Najeriya ya ruwaito cewa,
Kwamishinan ya ziyarci jihar Kano ne domin halartar wai taro na inganta
zamantakewar kananan yara. A yayin haka kuma kwamishinan ya yi kira ga al'ummar
jihar akan ci gaba d agoyon bayan gwamnan Abdulaziz yari da ta shugaban kasa
Muhammadu domin samun karsashi na sauke masu nauyin da rataya a wuyan su.
Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> whatsapp://chat?code=41x2TuRqdVQ9PrcrucqpTu
Shiga cikakken shafin mu kai tsaye www.isyaku.com
Tuntube mu ta SMS ko TEXT kawai zuwa 08087645001 ba mu amsa kira
Hausa.naij.ng
Tags:
LABARI