Turaki, babban lauya mai lambar SAN,
ya ce ya fi Buhari cancanta ne saboda ya fi shi ilimin boko. Tsohon minista a
lokacin mulkin jam'iyyar ta PDP karkashin Goodluck Jonathan, Tanimu Turaki na
daga cikin mutane 7 da suka bayyana sha'awar takara domin gwabzawa da shugaba
Buhari.
Turaki, Dan asalin jihar Kebbi, ya
bayyana cewar akwai fahimtar juna tsakanin masu son yiwa jam'iyyar ta PDP
takara, a saboda haka ya ce ba za a fuskanci kowacce matsala ba duk wanda a
karshe ya samu nasarar a zaben fitar da dan takara. A shekarar 2015 ne
jam'iyyar APC ta kayar da gwamnatin PDP bayan ta shafe 16 tana mulkin Najeriya.
Jam'iyyar PDP na saka ran sake
komawa kan karagar mulkin Najeriya a zaben shekarar 2019 mai zuwa. 'Yan
jam'iyyar APC mai mulki na cigaba tsallakawa zuwa jam'iyyar PDP, wani lamari
dake karawa jam'iyyar ta PDP karfin gwuiwar ganin cewar zata iya samun nasara a
zaben na shekarar 2019.
Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> whatsapp://chat?code=41x2TuRqdVQ9PrcrucqpTu Latsa nan domin ka sauke Manhajarmu ISYAKU.APK https://docs.google.com/uc?export=download&id=0B7lmLLhGZSx5OTVENFlsTkllRTQ Shiga cikakken shafin mu kai tsaye www.isyaku.com Tuntube mu ta SMS ko TEXT kawai zuwa 08087645001 ba mu amsa kira
Hausa.naij.ng