Sudan ta ce wajibi ne ta ci gaba da taya Saudiyya yakar Shi'a a Yaman

Ma'aikatar Tsaro ta Sudan ta bayyana cewa, wajibi ne ta ci gaba da taya Saudiyya kai hare-hare a Kasar Yaman wanda hakan wanibangare ne na cika halayyarta mai kyau.

Sanarwar ta rawaito ganawar Ministan tsaro na Sudan Ahmad Awad ibn Awf ya yi da Mataimakin Ministan Tsaron Saudiyya Muhammad Al-Ayash da ya ziyarci Khartoum inda ya gana da Shugaban Sudan Umar Al-Bashir da kuma Ministan tsaron kasar.

A ranar 7 ga watan Afrilu kakakin 'yan ta'addar Houthi 'yan Shi'a ya sanar da cewa, an kashe sojojin Sudan da dama a garin Midi na yankin Hajjaj da ke Kasar ta Yaman.

Amma Hukumomin Saudiyya ko na Sudan ba su tabbatar da wannan magana da kakakin 'yan ta'addar ya yi ba.
Tun shekarar 2014 yaman ta fada yakin basasa bayan da 'yan ta'addar Houthi suka kwace iko da San'a Babban Birnin Kasar. tare da yunkurin kwace gwamnati.

Don samun labaranmu ta Whatsapp ka rubuto YES a SMS zuwa 08087645001. Shiga cikakken shafinmu. www.isyaku.com

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN