Type Here to Get Search Results !

Main event

Sudan ta ce wajibi ne ta ci gaba da taya Saudiyya yakar Shi'a a Yaman

Ma'aikatar Tsaro ta Sudan ta bayyana cewa, wajibi ne ta ci gaba da taya Saudiyya kai hare-hare a Kasar Yaman wanda hakan wanibangare ne na cika halayyarta mai kyau.

Sanarwar ta rawaito ganawar Ministan tsaro na Sudan Ahmad Awad ibn Awf ya yi da Mataimakin Ministan Tsaron Saudiyya Muhammad Al-Ayash da ya ziyarci Khartoum inda ya gana da Shugaban Sudan Umar Al-Bashir da kuma Ministan tsaron kasar.

A ranar 7 ga watan Afrilu kakakin 'yan ta'addar Houthi 'yan Shi'a ya sanar da cewa, an kashe sojojin Sudan da dama a garin Midi na yankin Hajjaj da ke Kasar ta Yaman.

Amma Hukumomin Saudiyya ko na Sudan ba su tabbatar da wannan magana da kakakin 'yan ta'addar ya yi ba.
Tun shekarar 2014 yaman ta fada yakin basasa bayan da 'yan ta'addar Houthi suka kwace iko da San'a Babban Birnin Kasar. tare da yunkurin kwace gwamnati.

Don samun labaranmu ta Whatsapp ka rubuto YES a SMS zuwa 08087645001. Shiga cikakken shafinmu. www.isyaku.com

Post a Comment

0 Comments
* Please Don't Spam Here. All the Comments are Reviewed by Admin.

Top Post Ad

Below Post Ad

Shiga group dinmu na WhatsApp domin samun labaran mu kai tsaye LATSA NAN
Domin zama Wakilin mu a garin ku LATSA NAN
Domin aiko Sako/Labari/Korafi LATSA NAN
Domin samun labaran mu a Facebook LATSA NAN
Domin samun labaranmu a Twitter LATSA NAN

Hollywood Movies