An gano Saudiyya na bayar da taimako ga 'yan ta'addar PKK/PYD-YPG da ke arewacin Siriya

Saudiyya na bayar da taimako ga Kungiyoyin Larabawa da suke aiki tare da 'yan taa'addar aware na PKK/PYD-YPG a arewacin Siriya.

Ofishin Kamfanin dillancin labarai na Anadolu da ke garin Haseke ya bayyana cewa, aranar Juma'ar da ta gabata wasu manyan jami'an sojin Saudiyya 3 sun je garin Kobani tare da gana wa da 'yan ta'addar na PKK/PYD-YPG a sansanin Harap Ishk na sojin Amurka.

An samu labarin cewa, Saudiyya da Hukumominta na taimaka wa kungiyar ne don samar da wata runduna ta Larabawa mai karfi.

Saudiyya ta yi alkawarin biyan dala 200 kowanne wata ga duk wadanda suka amince da shiga rundunar inda tuni ta kafa cibiyoyi a Haseke da Kamishli.

A watan da ya gabata Saudiyya ta aike da kayan taimako a tireloli ga 'yan ta'addar PKK/PYD-YPG da ke arewacin Iraki. Akwai magunguna da makamai da ma motocin daukar marasa lafiya, amma gwamnatin Saudiyya ba ta ce komai game da batun ba.

A watan Oktoban shekarar da ta gabata ministan Saudiyya mai kula da harkokin yankjin Gulf ya ziyarci jami'an Amrka da ke yankin Rakka da 'yan ta'addar na PKK/PYD-YPG suka mamaye.

Don samun labaranmu ta Whatsapp ka rubuto YES a SMS zuwa 08087645001. Shiga cikakken shafinmu. www.isyaku.com

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN