Type Here to Get Search Results !

An gano Saudiyya na bayar da taimako ga 'yan ta'addar PKK/PYD-YPG da ke arewacin Siriya

Saudiyya na bayar da taimako ga Kungiyoyin Larabawa da suke aiki tare da 'yan taa'addar aware na PKK/PYD-YPG a arewacin Siriya.

Ofishin Kamfanin dillancin labarai na Anadolu da ke garin Haseke ya bayyana cewa, aranar Juma'ar da ta gabata wasu manyan jami'an sojin Saudiyya 3 sun je garin Kobani tare da gana wa da 'yan ta'addar na PKK/PYD-YPG a sansanin Harap Ishk na sojin Amurka.

An samu labarin cewa, Saudiyya da Hukumominta na taimaka wa kungiyar ne don samar da wata runduna ta Larabawa mai karfi.

Saudiyya ta yi alkawarin biyan dala 200 kowanne wata ga duk wadanda suka amince da shiga rundunar inda tuni ta kafa cibiyoyi a Haseke da Kamishli.

A watan da ya gabata Saudiyya ta aike da kayan taimako a tireloli ga 'yan ta'addar PKK/PYD-YPG da ke arewacin Iraki. Akwai magunguna da makamai da ma motocin daukar marasa lafiya, amma gwamnatin Saudiyya ba ta ce komai game da batun ba.

A watan Oktoban shekarar da ta gabata ministan Saudiyya mai kula da harkokin yankjin Gulf ya ziyarci jami'an Amrka da ke yankin Rakka da 'yan ta'addar na PKK/PYD-YPG suka mamaye.

Don samun labaranmu ta Whatsapp ka rubuto YES a SMS zuwa 08087645001. Shiga cikakken shafinmu. www.isyaku.com

Post a Comment

0 Comments
* Please Don't Spam Here. All the Comments are Reviewed by Admin.

Top Post Ad

Below Post Ad

Shiga group dinmu na WhatsApp domin samun labaran mu kai tsaye LATSA NAN
Domin zama Wakilin mu a garin ku LATSA NAN
Domin aiko Sako/Labari/Korafi LATSA NAN
Domin samun labaran mu a Facebook LATSA NAN
Domin samun labaranmu a Twitter LATSA NAN