Type Here to Get Search Results !

Main event

Za a yi bincike kan zargi da T.Y Danjuma ya yi wa sojin Najeriya - Buratai

Shugaban rundunar kasa na sojin Najeriya Lt. Gen Tukur Buratai ya kafa wani kwamiti wanda zai yi bincike a kan zargi da tsohon janar na soji T.Y Danjuma ya yi dangane da rikicin jihar Taraba.

A watan da ya gabata ne T.Y Danjuma ya zargi sojin Najeriya da aikata ba daidai ba a Taraba da Benue da kuma wasu sassa na Najeriya.

Danjuma ya zargi sojin Najeriya da mara wa masu kisan mutane baya a jihar Taraba tare da nuna goyon baya ga wani bangare a rikicin na Taraba.

Gen. Baratai ya ce wajibi ne a gudanar da bincike domin a tsabtace mutunci da darajar rundunar sojin Najeriya kuma bai kamata a yi fatali da irin wannan zargi ba.

Tuntube mu ko aiko Labari zuwa isyakulabari@gmail.com Don samun labaranmu ta Whatsapp ka rubuto YES a SMS zuwa 08087645001. Shiga cikakken shafinmu. www.isyaku.com

Top Post Ad

Below Post Ad

Shiga group dinmu na WhatsApp domin samun labaran mu kai tsaye LATSA NAN
Domin zama Wakilin mu a garin ku LATSA NAN
Domin aiko Sako/Labari/Korafi LATSA NAN
Domin samun labaran mu a Facebook LATSA NAN
Domin samun labaranmu a Twitter LATSA NAN

Hollywood Movies