Za a yi bincike kan zargi da T.Y Danjuma ya yi wa sojin Najeriya - Buratai

Shugaban rundunar kasa na sojin Najeriya Lt. Gen Tukur Buratai ya kafa wani kwamiti wanda zai yi bincike a kan zargi da tsohon janar na soji T.Y Danjuma ya yi dangane da rikicin jihar Taraba.

A watan da ya gabata ne T.Y Danjuma ya zargi sojin Najeriya da aikata ba daidai ba a Taraba da Benue da kuma wasu sassa na Najeriya.

Danjuma ya zargi sojin Najeriya da mara wa masu kisan mutane baya a jihar Taraba tare da nuna goyon baya ga wani bangare a rikicin na Taraba.

Gen. Baratai ya ce wajibi ne a gudanar da bincike domin a tsabtace mutunci da darajar rundunar sojin Najeriya kuma bai kamata a yi fatali da irin wannan zargi ba.

Tuntube mu ko aiko Labari zuwa isyakulabari@gmail.com Don samun labaranmu ta Whatsapp ka rubuto YES a SMS zuwa 08087645001. Shiga cikakken shafinmu. www.isyaku.com
Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN