Ko an shirya kenan tsakanin Korea ta Kudu da ta Arewa ?

Shugaban kasar Koriya ta Arewa Kim Jong-un ya ziyarci takwaransa na Koriya ta Kudu Moon Jae-in lamarin da ake ganin zai kafa tarihin samar da zaman lafiya da lumana a tsakanin kasashen biyu.

Shugabanin biyu sun gana a Panmunjom da suka kira kauyen zaman lafiya domin tattunawa akan samar da zaman lafiya a tsakaninsu inda shugaba Kim ya rataba hannu a cikin littafin lumana da aka bude.

Kim ya bayyana cewar yanzu mun fara daukar matakan samar da zaman lafiya a tsakanimu kuma zamu mutunta matakan da zamu dauka.

A watan Febrairu shugaba Kim ya tura wasu tawagar da suka kunshi har da kaunarsa Kim Yo-jong zuwa Koriya ta Kudun inda suka fara tattauna samar da zaman lafiya tsakanin kasashen biyu.

A taron zaman lafiyar, shugaban Koriya ta Arewa ya bayyana irin farin cikinsa akan ganawa da takwaransa na Koriya ta Kudu da yayi ,inda ya kara da cewa yanada yakinin taron zai haifar da da mai ido.

Shugabanin biyu sun godewa juna akan gudanar da taron inda dukkaninsu suka nuna farin jikinsu akan matakan samar da lumana a tsakaninsu.

Moon ya bayyana cewar al'umar kashashen biyu dama duniya baki daya sun karkata kunnuwansu da idanuwansu zuwa Panmunjom domin kowa na bukatar nasarar taron da ake gudanarwa.

Hakika, nasarar wannan taron zai kasance tamkar wata babbar kyauta ga al'umar kasashen dama duniya baki daya.

Don samun labaranmu ta Whatsapp ka rubuto YES a SMS zuwa 08087645001. Shiga cikakken shafinmu. www.isyaku.com

Daga TRT 
Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN