Mai taimaka wa shugaba Muhammadu Buhari ta fannin sadarwa Femi Adesina ya ce zance da shugaban ya yi a shekara ta 2011 cewa zai yi shugabanci ne na shekara hudu kacal idan ya ci zabe baya da tasiri a yanzu.
A wata hira da ya yi da gidan talabijin na Channels TV da safiyar Talata, Adesina ya ce shugaba Buhari ya yi wannan furuci ne a waccan lokaci kuma ya yi takara ya fadi a waccan zaben.
Ya kara da cewa a wannan lokaci ai shugaban bai yi wannan alkawari ba. Kuma nassarar lashe zabe a shekara ta 2015 ne ba 2011 ba.
Tuntube mu ko aiko Labari zuwa
isyakulabari@gmail.com
Don samun labaranmu ta Whatsapp ka rubuto YES a SMS zuwa 08087645001.
Shiga cikakken shafinmu.
www.isyaku.com