Yadda birai suka kwace ragamar wata al'umma a Lagos

Mazauna unguwar Soluyi-Sosanya a Gbagada na jihar Lagos sun bukaci hukumomi su kawo masu dauki bayan goggon birai sun addabe su a gidajensu kuma suka hana su sakat.

Shugaban masu gidajen haya na unguwar Mr. Adigun Olaleye ya ce biran sukan fito ne daga wani daji da ke kusa da unguwrar kuma sukan shiga gidaje ba sallama ta hanyar fadowa cikin gidaje da dakunan mutane.

Ya ce sakamakon haka biran sukan yi barna ta hanyar karya kujeri,da duk wani abin da suka gani a cikin gidaje.

Daga karshe Mr. Adigun Olaleye ya bukaci hukumomi su taimaka a kori biran ko a kama su.

Tuntube mu ko aiko Labari zuwa isyakulabari@gmail.com Don samun labaranmu ta Whatsapp ka rubuto YES a SMS zuwa 08087645001. Shiga cikakken shafinmu. www.isyaku.com
Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN