Rundunar sojin Najeriya ta musanta rahotannin da ke cewa jagoran mayakan Boko Haram Abubakar Shekau ya tsere zuwa kasar Kamaru.
Kakakin rundunar sojin kasar
Birgediya Janar Sani Usman Kukasheka, ya ce sojin Najeriya basu da
masaniya kan inda Shekau ya ke, sabanin yadda wasu rahotanni suka ce,
wani babban kwamandan kungiyar Boko Haram da suka kama, a ranar 14 ga
watan Fabarairu, ya shaida musu cewar Shekau ya tsere zuwa Kamaru,
hasalima basa tsare da kwamandan da aka kira da Abu Zainab.
A karshen makonnan ne rundunar sojin Najeriya, ta yi shelar bada kyautar naira miliyan 3, ga duk wanda ya taimaka da bayanai wajen gano maboyar jagoran kungiyar ta Boko Haram Abubakar Shekau.
A farkon makon watan Fabarairu, jagoran kungiyar ta Boko Haram Abubakar Shekau ya fitar da wani sabon sako na bidiyo, in da yake cewa ya gaji da masifar da suke fuskanta kuma ya gwammace mutuwarsa don hanzarta shiga aljanna.
A karshen makonnan ne rundunar sojin Najeriya, ta yi shelar bada kyautar naira miliyan 3, ga duk wanda ya taimaka da bayanai wajen gano maboyar jagoran kungiyar ta Boko Haram Abubakar Shekau.
A farkon makon watan Fabarairu, jagoran kungiyar ta Boko Haram Abubakar Shekau ya fitar da wani sabon sako na bidiyo, in da yake cewa ya gaji da masifar da suke fuskanta kuma ya gwammace mutuwarsa don hanzarta shiga aljanna.
Tuntube mu ko aiko Labari zuwa isyakulabari@gmail.com Don samun labaranmu ta Whatsapp ka rubuto YES a SMS zuwa 08087645001. Shiga cikakken shafinmu. www.isyaku.com
Daga rfi
Tags:
LABARI