Masu yin kabbara su kashe mutane jahannama zasu shiga ba aljanna ba - Sultan


Sarkim Musulmi Alhaji Muhammad Sa’ad Abubakar III yace wadanda ke yin kabbara su kashe mutane da tunanin cewa zasu shiga Aljanna sun yi kuskure domin zasu shiga wutan Jahannama ne.
Sarkin Musulmi yayi wannan jawabi ne a wajen taro na 9 domin mutunta darajar 'dan adam a jami'ar Najeriya da ke Nsukka.

Basaraken yace wadanda ke kashe mutane tare da tunanin cewa suna yin aikin Allah ne suna yaudaran kansu ne domin Allah baya lamuntar zubar da jinin bil'adama ko da ba Musulmi bane.

Haka zalika Sultan Abubakar yace duk wata al'umma da bata mutunta rayuwar dan'adam ba al'umma ce da ta waye ba.Ya kuma kara da cewa babu yadda Fulani makiyayi zai kashe dan adam domin ya kare ran shanu,saboda haka masu aikata laifi ne ke kashe mutane amma ba Makiyaya masu kiwon shanu ba.

Ga masu shawara,aiko labari ko korafi ku rubuto zuwa isyakulabari@gmail.com Kaunace mu a Facebook https://www.facebook.com/isyakuweb Don samun labaranmu ta Whatsapp ka rubuto YES a SMS zuwa 08087645001. Shiga cikakken shafinmu. www.isyaku.com

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN