Cutar kyandan biri ta yadu zuwa jihar Rivers da Akwa Ibom

An sami bullar cutar kyandan biri a jihar Akwa Ibom, wani babban jami'in Gwamnatin jihar yace akalla mutum 13 suna kwance a Asibiti a jihohin Bayelsa da Rivers da ke makwabtaka da jihar Akwa Ibom.

A wata sanarwa da ya fitar a Uyo, kwamishinan yada labarai na jihar Charles Udoh ya bayyana bullar cutar inda ake wa mutum daya magani yayin da Gwamnati ke ci gaba da bincike akan cutar.

Kwamishinan ya kara da cewa cutar ta kyandan biri yayi kama da cutar kyanda da aka saba da shi,yace banbancin cutar shine kuraje na kyandan biri sun fi girma bisa ga kurajen kyanda na asali.


Ga masu shawara,aiko labari ko korafi ku rubuto zuwa isyakulabari@gmail.com Kaunace mu a Facebook https://www.facebook.com/isyakuweb Don samun labaranmu ta Whatsapp ka rubuto YES a SMS zuwa 08087645001. Shiga cikakken shafinmu. www.isyaku.com

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN