Asirin dan boko haram ya tonu kafin ya kai hari

 'Yan sanda a jihar Ondo sun kama wani 'dan kungiyar boko haram Muhammed Bashir a Isua Akoko hedikwatar Akoko ta gabas a jihar Ondo wadda bayanai suka nuna cewa kungiyar tana shirin kai hari a jihar Ondo kafin a cafke Muhammed.

Kwamishinan 'yansanda na jihar Ondo Mr. Gbenga Adeyanju ya shaida wa manema labarai haka ranar Talata inda ya kara da cewa rundunarsa zata mika 'dan boko haram din ga Soji domin ci gaba da bincike.

Muhammed wadda yayi jawabi da Hausa ya shaida wa Manema labarai cewa ya shiga kungiyar ne watannin baya kuma mutum biyu ne kawai ya taba kashewa,wani yaro da ya kashe a cikin daji sai wani mutum da ya harbe a gefen hanya.

Ya kara da cewa akwai 'yan kungiyar ta boko haram da suka tsere zuwa jihar Ondo sakamakon matsin lamba daga soji.Ya ce shi mazauni jihar Nassarawa ne kafin ya tsere zuwa jihar Ondo.

Ga masu shawara,aiko labari ko korafi ku rubuto zuwa isyakulabari@gmail.com Kaunace mu a Facebook https://www.facebook.com/isyakuweb Don samun labaranmu ta Whatsapp ka rubuto YES a SMS zuwa 08087645001. Shiga cikakken shafinmu. www.isyaku.com

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN