DSS ta kama wadanda suka shirya kai hari lokacin Sallar Layya a wasu jihohi

Hukumar ayyukan tsaro da leken asiri na cikin gida DSS ta yi nassarar cafke wasu masu tsastsaurar ra'ayin Islama da suka shirya kai hare hare a lokacin bukukuwan Sallar Layya da ya gabata.

Sanarwar hakan ya fito daga hannun mai magana da yawun hukumar Mr Tony Opuiyo wadda ya ce 'yan ta'addan sun shirya kai hare-haren ne a Abuja, Kano, Kaduna, Niger, Bauchi, Yobe da Borno.

Opuiyo yace wadanda aka kama sun shirya akan zasu yi amfani da bama-bamai da kisan kan mai uwa da wabi ta hanyar yin amfani da bindigogi masu sarrafa kansu domin su buda wuta a wajajen cinkoso na jama'a lokacin shagul gular Sallah.

Rundunar ta ce ta yi nassarar damke wani  Moses Peverga a Abuja wadda shi ne ke samar da makamai ga bata gari a jihar Benue lamarin da ya sa ake samun aikata mugan laifuka ta hanyar yin amfani da makaman.

Haka zalika rundunar ta cafke Abdulkadir Mohamm, Muhammad Ali, da Husseini Mai-Tangaran a birnin Kano bisa zargin su da kitsa shirin hari da akayi niyyar kaiwa lokacin bukukuwan Sallar Layya a birnin Kano da kewaye.

Kaunace mu a Facebook https://www.facebook.com/isyakuweb Don samun labaranmu ta Whatsapp ka rubuto YES a SMS zuwa 08087645001. Shiga cikakken shafinmu. www.isyaku.com

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN