Yara 'yan Aji 6 a firamare ba su iya karatun fatiha ba .Wannan ya faru ne a wata makaramta a wani Kauye da ake Kira "Sakace" a karamar hukumar Mulki ta shanga.
A lokacin da na shiga aji shidda domin tabbatar da wannan, na nemi wasu daliban su karanta mini wani abu a cikin Qur'ani sai suka kasa !
Daga nan ne na nemi su karanta mini "suratul fatiha" wallahi ban samu yaro ko daya da ya iya karantawa ba !
Wannan yasa na kalubalanci Malamin da yake koyar da wannan darasin cewa ya akayi hakan ya faru ?
Yace shima baijima da zuwa ba haka ya tarar da su , kuma yana iya kokarinsa akan wannan matsalar.
To abin tambaya anan shine:
Ya akayi yaro zai kai aji shidda amma bai iya fatiha ba ?
Laifin waye a cikin wadannan ?
1 Gwamnati
2 Iyaye,
3 Shugaban Makaranta (Head Master)
4 Malaman Makaranta
Daga Sani Musa Saminaka
Ku biyo mu a
https://www.facebook.com/isyakuweb
Don samun labaranmu ta Whatsapp ka rubuto YES a Whatsapp zuwa 08062543120 zamu aiko maka da Labaran mu kai tsaye.
Don aiko Labari ko korafi ka tuntube mu a 08062543120.
Shiga www.isyaku.com Don samun cikakken shafinmu da ke dauke da ababe masu kayatarwa.
Tags:
LABARI