Yara 'yan aji 6 a firamare ba su iya karatun fatiha ba.

Yara 'yan Aji 6 a firamare ba su iya karatun fatiha ba .Wannan ya faru ne a wata makaramta a wani Kauye da ake Kira "Sakace" a karamar hukumar Mulki ta shanga. 

A lokacin da na shiga aji shidda domin tabbatar da wannan, na nemi  wasu daliban su karanta mini wani abu a cikin Qur'ani sai suka kasa !

Daga nan ne na nemi su karanta mini  "suratul fatiha"  wallahi ban samu yaro ko daya da ya iya karantawa ba !
Wannan yasa na kalubalanci Malamin da yake koyar da wannan darasin cewa ya akayi hakan ya faru ?

Yace shima baijima da zuwa ba haka ya tarar da su , kuma yana iya kokarinsa akan wannan matsalar.
To abin tambaya anan shine:

Ya akayi yaro zai kai aji shidda amma bai iya fatiha  ba ?

Laifin waye a cikin wadannan ? 

1  Gwamnati

2  Iyaye,

3  Shugaban Makaranta (Head Master) 

4  Malaman Makaranta


Daga Sani Musa Saminaka




Ku biyo mu a
https://www.facebook.com/isyakuweb
Don samun labaranmu ta Whatsapp ka rubuto YES a Whatsapp zuwa 08062543120 zamu aiko maka da Labaran mu kai tsaye.
Don aiko Labari ko korafi ka tuntube mu a 08062543120.
Shiga www.isyaku.com Don samun cikakken shafinmu da ke dauke da ababe masu kayatarwa.

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN