Emmanuel Macron ya kama aiki a matsayin sabon shugaban Faransa

Sabon shugaban Faransa Emmanuel Macron ya sha alwashin maido da kimar kasar a idon duniya, wadda ke fuskantar baranazar gushewa a baya.
Macron mai shekaru 39, ya yi alkawarin ne a lokacin bikin rantsar da shi a matsayin sabon shugaban kasar ta Faransa, da ya gudana yau Lahadi a birnin Paris, sati guda bayan nasarar da yayi kan Marine Le Pen, a zaben shugabancin kasar zagaye na biyu a ranar 7 ga watan da muke ciki, da kashi 65 na kuri’un da aka kada.Daga cikin manyan batutuwan da Macron yace gwamnatinsa zata fi bai wa muhimmanci akwai sabunta tsare tsaren tafiyar da fannin tsaron kasar, yin garambawul a fannin kwadago, sai kuma jagorantar sake saita ginshikan da suka kafa kungiyar tarayyar turai EU.

Macron da ya kuma yi alwashin daukaka ‘yancin Faransawa da dimokaradiyyar kasar, ya zama shugaban kasa mafi karancin Shekaru a tarihin kasar tun bayan Napoleon Bonoparte.

A gobe Litinin ake sa ran sabon shugaba Macron, ya bayyana sunan Firaministan da zasu yi aiki tare, kafin ziyara ta farko bayan rantsar da shi, da zai kai wa shugabar gwamnatin Jamus Angela Markel a birnin Berlin.
Ana sa ran batutuwan da suka hada da, karfafa turakun da suka kafa kungiyar tarayyar turai EU, da kuma fannin tsaro su mamaye tattaunawar da shugabannin biyu zasu yi.

 
@isyakuweb  https://web.facebook.com/isyakuweb
 

Wannan labarin ya fara baiyana a shafin RFI

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN