Mugunta: Wata Mata ta kulle yara 3 a wani daki da niyyar kashe su da yunwa

Wata mata wadda kishiya ce ga uwar wasu yara da ubansu ya auro ta kulle yaran su uku a cikin wani daki a gidan kuma babu abinci ko ruwan sha da niyyar cewa yaran su mutu da yunwa a cikin birnin Kano..

Majiyar mu ta labarta mana cewa hakan ya farune bayan uban yaran yayi balaguro,sai wannan matar ta aikata wannan aika-aikan.Babu cikakken bayani ko kwana nawane yaran suka yi a kulle.

Makwabta sun lura da abin da ke faruwa bayan yaran sunyi ta sheka ihu,tuni dai bala'in yunwa da kishin ruwa ya baiyana a jikin wadannan yaran bayin Allah kafin makwabta su cece su.

Bayanai sun nuna cewa an gabatar da matsalar gaban hukumomin tsaro a jihar ta Kano.


@isyakuweb  https://web.facebook.com/isyakuweb

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN