Kamar yadda muka yi bayani a baya,alokacin da jami’an NAIC
suka kama aikin tsaron lafiyar shugaba Buhari tare da hadin gwuiwan jami’an DSS
wanda aikin su ne a bisa asali da ka’ida su tsare lafiyar shugaban kasa,hakan
ya haifar da gibi na rashin yarda da kuma iya fahimtar me kake nufi ko kuma me
zaka yi.Saboda kowa yana yiwa dan uwansa kallon kallo.
Marmakin a mayarda hankali wajen kare lafiyar shugaban kasa
a bisa akida da tsarin mulki ya shimfida sai aka dawo ana nuna takama da karfin
iko,ta hanyar nuna ko ni nafika ko kai baka isa ba domin hurumi na ne tun
asali.A bisa nazari na ka’idodin tsaron lafiyar shugaba,wannan wani kuskure ne
da zai iya haifar da gibi da makiya zasu samu saboda su cutar da shugaban kasa.
Wasu daga cikin wasu jami’ai da suka shigo cikin jerin masu
tsaron lafiyar shugaban kasa,bincike da muka gudanar ya nuna cewa basu sami horo
irin wanda ake bayarwa ba don tsaron lafiyar shugaban kasa.A bisa wannan dalili
ne za’a iya samun sakaci da makiyi zai iya samu domin ya kutsa kanshi har yayi
ido biyu da shugaban kasa kuma ya cutar da shi cikin sauki,saboda rashin
kwarewar jami’i wajen tantance take taken bako ko ma’aikacin gida ko kuma
munafukin jami’in tsaro.
Matsawar za’a jagula tsarin ka’ida da gaskiya da tsari na
son ra’ayi a wajen harkar kare lafiyar shuganni a Najeriya,akwai fargaban cewa karshen
lamarin shine hakan zai iya haifar da mummunar sakamako da zai haifar da
danasani ga wadanda abin ya shafa.
1.Daga karshe,ina ba mahukuntar Najeriya shawara akan cewa
wajibi ne a bar jami’an DSS su tafiyar da aikin sun a tsaron lafiyar shugaba Buhari
a matsayin jami’an kariya na zoben farko na tsaro.
2.Wajibi ne zobin tsaro na farko ya kasance jami’an DSS,
sune masu bayar da jikin su domin dakile duk wani barazana da ido zai iya gani
a matakin farko.
3.Zoben tsaro na biyu dole ne ya kasance jami’an na DSS
saboda su ne masu yunkurin daukan mataki na gaggawa domin a janye shugaba daga
wajen da aka fuskanci barazana zuwa wajen da ake zaton ya kasance tudun na
tsira.Jami’ai ne da suke da horo na musamman akan matsayin su da kuma rawar da
zasu taka a wajen tsaron lafiyar shugaban kasa,kuma sun sami horo daga
hukumomin leken asiri na wasu manyan kasashen duniya da Amurka,Ingila da Isra’ila.
4.Zoben tsaro na uku shima DSS ne ya kamata ta rike,domin
aikin wannan zoben shine samar da zaratan jami’an na DSS wanda aka basu horo na
musamman kuma ake kira daya tamkar 20.Wadannan jami’an na DSS an basu
wadataccen horo daga wasu hukumomin liken asiri na wasu kasashe kamar Musad na
Isra’ila da hukumar leken asiri na Britaniya MI6 da kuma hukumar ayyukan asiri
na Amurka (American Secret Service).Aikin wadannan jami’ai shine su mayar da
wadataccen martini ga duk wanda ya tunkaro fadar da wata barazana musamman wanda
ya shafi amfani da makami.
5.Wannan zoben shi ne ya shafi sauran jami’an tsaro da ake
turawa fadar shugaban kasa ,amfanin su shine su bayar da Karin gudunmawa koda
za’a fuskanci wata barazana.Wannan zoben shine ya kunshi jami’an NAIC,‘Yan
sandan kwantar da tarzoma,Sojoji da jami’an Civil defence,FRSC da Fire service.
Daga karshe,kuskuren da aka samu shine duk wadannan ka’idodin
an yi fatali dasu,sai ka gan jami’in day a kamata a zobe na biyar ya kutsa
kanshi zuwa mataki na zobe na uku,wanda ke a matakin zobe na biyu an dawo da shi
zuwa matakin zobe na hudu.Yanzu kai mai karatu,don Allah yaya zaka yanke
hukunci a wannan tsari idan aka baka Alkalanci akan ko laifin waye ya sa aka
bari aka sanya guba a bututun AC na dakin shugaban kasa?