Kamaru ta yi waje da Ghana a gasar Afrika

Tawagar kwallon kafa ta Kamaru ta fitar da Ghana daga gasar cin kofin nahiyar Afrika da ake gudanarwa a Gabon bayan sun tashi wasa da ci 2-0 a fafatawarsu ta jiya a birnin Franceville.
Kamaru ta samu nasarar zura kwallayen ne bayan dawowa daga hutun rabin lokaci, in da Michael Ngadeu-Ngadjui ya zura kwallon farko a minti na 72, yayin da Christian Bassogog ya zura ta biyu a minti na 93.
A ranar Lahadi mai zuwa ne Kamaru za ta kara da Masar a matakin wasan karshe na wannan gasar ta cin kofin Afrika wadda ita ce, karo na 31.
Kocin Kamaru Hugo Broos ya ce, burinsu na zuwa matakin wasan karshe ya cika duk da cewa, Ghana ta fi su kwarewa wajen murza tamaula.
RFI

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN