MARTANIN 'YAN SHI'A GA SAKON BUHARI NA SABUWAR SHEKARA

Magoya bayan Ibrahim Zakzaki a Najeriya sun mayarwa shugaba Muhammadu Buhari da martani bayan a cikin sakon shi na sabuwar ya bukaci mabiyan na Shi’a su rungumi zaman lafiya tare da bin dokokin kasa.
A sakon da ya aike wa al’ummar kasar dangane da shiga sabuwar shekara ta 2017 shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya bukaci mabiya Shi’a da kuma wadanda ke dauke da makamai a yankin Niger Delta da su rungumi zaman lafiya, sannan kuma su kasance masu mutunta dokokin kasar.
Amma Ibrahim Musa Kakakin ‘yan Shi’ar a Najeriya, ya ce dama su mutane ne masu kaunar zaman lafiya.
"Duk da kisan da aka yi wa mutanenmu amma ba mu dauki doka a hannunmu ba, muna ci gaba da bin hanyoyi na lamama". a cewar Ibrahim Musa Al Mizan.
‘Yan Shi’ar sun ce Shugaba Buhari ne suke bukatar ya kasance mai bin doka da oda bayan Kotu ta bayar da umurnin a saki jagoransu.
(RFI )

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN