Magoya bayan Ibrahim Zakzaki a Najeriya sun
mayarwa shugaba Muhammadu Buhari da martani bayan a cikin sakon shi na
sabuwar ya bukaci mabiyan na Shi’a su rungumi zaman lafiya tare da bin
dokokin kasa.
A sakon da
ya aike wa al’ummar kasar dangane da shiga sabuwar shekara ta 2017
shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya bukaci mabiya Shi’a da kuma
wadanda ke dauke da makamai a yankin Niger Delta da su rungumi zaman
lafiya, sannan kuma su kasance masu mutunta dokokin kasar.
Amma Ibrahim Musa Kakakin ‘yan Shi’ar a Najeriya, ya ce dama su mutane ne masu kaunar zaman lafiya.
"Duk da kisan da aka yi wa mutanenmu amma ba mu dauki doka a hannunmu ba, muna ci gaba da bin hanyoyi na lamama". a cewar Ibrahim Musa Al Mizan.
‘Yan Shi’ar sun ce Shugaba Buhari ne suke bukatar ya kasance mai bin doka da oda bayan Kotu ta bayar da umurnin a saki jagoransu.
(RFI )
Amma Ibrahim Musa Kakakin ‘yan Shi’ar a Najeriya, ya ce dama su mutane ne masu kaunar zaman lafiya.
"Duk da kisan da aka yi wa mutanenmu amma ba mu dauki doka a hannunmu ba, muna ci gaba da bin hanyoyi na lamama". a cewar Ibrahim Musa Al Mizan.
‘Yan Shi’ar sun ce Shugaba Buhari ne suke bukatar ya kasance mai bin doka da oda bayan Kotu ta bayar da umurnin a saki jagoransu.
(RFI )
Tags:
LABARI