AN KASHE MUTUM BIYU KUMA AKA KONA MASALLACI A ENUGU- BAYAN FILANI SUN SHA DUKA


Mutun biyu ne aka kashe bayan rikici ya barke tsakanin wasu Inyamirai da Filani a kasuwar Gariki a garin Enugu.Musabbabin rikicin  shine wai wani bafillace ne mai suna Ali ya je da saniyar sa zuwa Mayankar kasuwar kuma ana biyan N500 ne,sai Ali ya bayar da N400 marmakin N500,bayan ya gama fede saniyar komai ya kammala sai zai wuce,saboda haka mai kula da Mayankar mai suna Ifeanyi Ifeacho ya bukaci Ali ya cika sauran N100 da ya rage,wannan yanayin ne ya jawo kaurewar fada a tsakanin su,shi kuma Ali ya zaro wuka ya daba wa Ifeanyi a ciki inda ya mutu nan take.
Ganin hakar kee da wuya sai Ali yayi kokarin tserewa,jama'ar Inyamirai da suka harzuka suka bishi da gudu,ya sha duka har ya mutu,daga bisani Inyamiran suka auka w duk wani dan Arewa da ke garin kuma suka kona Masallacin kasuwar.

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN