Mutun biyu ne aka kashe bayan rikici ya barke tsakanin wasu Inyamirai da Filani a kasuwar Gariki a garin Enugu.Musabbabin rikicin shine wai wani bafillace ne mai suna Ali ya je da saniyar sa zuwa Mayankar kasuwar kuma ana biyan N500 ne,sai Ali ya bayar da N400 marmakin N500,bayan ya gama fede saniyar komai ya kammala sai zai wuce,saboda haka mai kula da Mayankar mai suna Ifeanyi Ifeacho ya bukaci Ali ya cika sauran N100 da ya rage,wannan yanayin ne ya jawo kaurewar fada a tsakanin su,shi kuma Ali ya zaro wuka ya daba wa Ifeanyi a ciki inda ya mutu nan take.
Ganin hakar kee da wuya sai Ali yayi kokarin tserewa,jama'ar Inyamirai da suka harzuka suka bishi da gudu,ya sha duka har ya mutu,daga bisani Inyamiran suka auka w duk wani dan Arewa da ke garin kuma suka kona Masallacin kasuwar.
Ganin hakar kee da wuya sai Ali yayi kokarin tserewa,jama'ar Inyamirai da suka harzuka suka bishi da gudu,ya sha duka har ya mutu,daga bisani Inyamiran suka auka w duk wani dan Arewa da ke garin kuma suka kona Masallacin kasuwar.
Tags:
LABARI