"Makiyaya su bar yankin mu kafin 1 ga Oktoba ko mu kaddamar da yaki" - Matasa

Wata kugiyar matasa karkashin hadaddiyar kungiyar matasan yankin tsakiyar Najeriya da ake kira "Middle Belt Renaissance Forum ta bukaci Makiyaya su fice daga yankin tsakiyar Najeriya da ake kira "Middle belt" kafin ranar 1 ga watan Oktoba ko ta kaddammar da yaki.

Sanarwar haka ya fito ne daga hannun shugaban hadaddiyar kungiyar matasan Comrade Jones Simon Alfa bayan kammala wani taro da sukayi a binin Abuja wanda majiyar mu ta shaida mana cewa ya sami halartar ilahirin wakilan kungiyoyin matasa da suka danganta kansu da tsakiyar Najeriya "Middle belt".

Comrade Jones ya kuma yi kira ga Gwamnonin yankin da cewa su mayar da hankali wajen biyawa talakkawa bukatun rayuwa ba wai su dinga farautar 'yan jarida ,marubuta,ma'abota amfani da shafin sada zumunta ba wajen sawa a tsare su saboda sun fadi gaskiya.


Ya kuma kara da cewa "Wajibi ne Makiyaya su fice daga yankin kafin wa'adin da suka bayar na 1 ga watan Oktoba ko su  kaddamar da yaki"


Ku biyo mu a https://www.facebook.com/isyakuweb Don samun labaranmu ta Whatsapp ka rubuto YES a Whatsapp zuwa 08062543120. Don aiko Labari ko korafi ka tuntube mu a 08062543120. Shiga www.isyaku.com Don samun cikakken shafinmu da ke dauke da ababe masu kayatarwa.

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN