Rabin matalauta na duniya na nahiyar Afirka | isyaku.com

Wani rahoto da aka fitar karkashin Kungiyar Hadin Kai ta Afirka a yayin babban taron raya al’adu da sna’o’in hannu da aka gudanar a birnin Kasabalanca na kasar Morokko ya bayyana cewa, rabin matalauta da ke duniya na a nahiyar Afirka.

A fadin duniya gaba daya a kwai mutane biliyan 1 da ke fama da yunwa, wato a duk mutum 9 na duniya 1 ba ya samun isasshen abincin da zai ci. Nahiyar Afirka ce ta fi kowacce fama da talauci da yunwa, kamar yadda kwararru suka bayyana. Kwararrun sun ce, rabin matalautan duniya na rayuwa a Afirka.

Daraktan Kungiyar Hadin Kai ta Afirka Dr. Siyogi Sifa ya jaddada cewa, kaso 41 cikin 100 na talakawan duniya na nahiyar Afirka.


@isyakuweb  https://web.facebook.com/isyakuweb

wannan labarin ya fara bayyana a shafin TRT

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN