Musulmai a kasashe daban-daban na
duniya ciki har da Najeriya za su fara azumin watan Ramadan ranar Asabar
bayan an sanar da ganin wata.
Mai alfarma sarkin Musulmi, wanda shi ne shugaban majalisar, Sultan Sa'ad Abubakar III, shi nne ya bayyana ganin watan a garuruwa daban-daban a Najeriya a wani taron manema labarai da aka gudanar a daren Juma'a.
Baya ga Najeriya Musulmai a wasu kasashen duniya irinsu Saudiyya da ma za su fara azumin na watan Ramadana ranar Asabar.
Ramadan dai wata ne mai alfarma ga musulmi inda ake matsa kaimi kan ibada da addu'o'i.
@isyakuweb https://web.facebook.com/isyakuweb
Tags:
SANARWA