Babban lauya Femi Falana, ya ce kundin tsarin mulkin Nijeriya ya ba
shugaba Buhari karfin ikon ci-gaba da aiki da Ibrahim Magu a matsayin
shugaban hukumar yaki da cin hanci da rashawa EFCC har
illa-masha-Allahu.
Falana, ya bayyana haka ne, yayin da ya ke jawabi a cikin shirin Sun Rise Daily da gidan talabijin na Chanels ke shiryawa, inda ya ce ba daidai ba ne a ce Magu ba zai iya ci-gaba da aiki ba don kawai majalisar dattawa ta ki tantance shi.
Lauyan ya kara da cewa, kamar yadda ya ke a sashe na 171 na kundin tsarin mulkin Nijeriya, akwai nade-naden da ba su bukatar shugaban kasa ya nemi amincewar wani.
Ya ce ‘yan majalisa su na da ‘yancin tantance jakadu da sauran hukumomin harkokin ketare ne kawai, kamar yadda ya ke kunshe a sashe na 171 sakin layi na 2 na kundin tsarin mulkin Nijeriya.
Liberty
@isyakuweb https://web.facebook.com/isyakuweb
Falana, ya bayyana haka ne, yayin da ya ke jawabi a cikin shirin Sun Rise Daily da gidan talabijin na Chanels ke shiryawa, inda ya ce ba daidai ba ne a ce Magu ba zai iya ci-gaba da aiki ba don kawai majalisar dattawa ta ki tantance shi.
Lauyan ya kara da cewa, kamar yadda ya ke a sashe na 171 na kundin tsarin mulkin Nijeriya, akwai nade-naden da ba su bukatar shugaban kasa ya nemi amincewar wani.
Ya ce ‘yan majalisa su na da ‘yancin tantance jakadu da sauran hukumomin harkokin ketare ne kawai, kamar yadda ya ke kunshe a sashe na 171 sakin layi na 2 na kundin tsarin mulkin Nijeriya.
Liberty
@isyakuweb https://web.facebook.com/isyakuweb
Tags:
LABARI