Soja ya kashe wata macen soja a kan zargin soyayya da wani


Wani sojan sama na Najeriya ya harbe abokiyar aikinsa itama sojar sama a wuya har lahira a bisa zargin cewa tana soyayya da wani mutum daban bayan shi.Sojan da ya aikata wannan laifi mai suna Kalu M.O ya fada hannun 'yan sandan sojan sama a barikin sojan sama da ke Makurdi a jihar Benue inda ake tsare da shi a bisa tuhumarsa da laifin kisan Macen sojan sama mai suna Sholape.

Rahotanni sun nuna cewa lamarin ya faru ne da karfe 4:36 na asuba a dakin wanda yayi kisan watau Kalu,kuma ita mariganyar ta kwana a dakin Kalu ne a ranar da abun ya faru saboda dama can budurwar shi ce da suka fara soyayya tun 2016.Bayanai sun nuna cewa Kalu yayi yunkuri domin ya kashe kanshi har ma ya rubuta takardar alamar cewa zai kashe kanshi amma sai ya kasa.


Wata majiya ta shaida wa ISYAKU.COM cewa idan aka sami Kalu da laifin kashe Mace sojan sama abokiyar aikin shi to lallai zai fuskanci hukuncin kisa ne ta hanyar daure shi a durom kuma a harbe shi har lahira shima.Wannan shari'ar dai Kotun musamman ta soja ce zata aiwatar da shi.

Isyaku Garba
@isyakuweb kubiyo mu a facebook
https://web.facebook.com/isyakuweb
Aiko da Labari

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN