JIRAGEN YAKIN NAJERIYA SUN JEFA BOM KAN FARAREN HULA "A BISA KUSKURE"

Mutane da dama ne ake fargabar sun rasa rayukansu bayan da jiragen yakin sojin Najeriya suka jefa bama-bamai bisa kuskure kan fararen hula a kauyen Raan a jihar Borno.
Rundunar sojin ta ce cikin wadanda lamarin ya rutsa da su, wanda ya faru a karamar hukumar Kale-balge, sun hada da jami'an lafiya na MSF da kungiyar agaji ta Red Cross.
Shugaban rundudar yaki da Boko Haram Manjo Janar Lucky Irabor ya shaida wa manema labarai cewa an samu mutuwa da raunuka a harin.
Ya kara da cewa har da sojoji a cikin wadanda suka jikkata.
Mai magana da yawun rundunar tsaro ta Najeriya Janar Rabe Abubakar ya shaida wa BBC cewa sun kadu kan wannan kuskure da ya faru.

Agajin gaggawa

Ya ce lamarin ya faru ne bayan sun samu labarin cewa mayakan Boko Haram sun taru a wani waje da shirin kai hari.
''Amma a bisa tsautsayi sai ya fada wannan kauye. Ba da niyya mu kai hakan ba, kuma hakan dama kan faru a yankunan da ake yaki,'' in ji Janar Rabe.
Jami'in ya jajanta kan lamarin inda kuma ya ce har yanzu ba a san adadin mutanen da suka mutu ba, ''amma muna ci gaba da bincike,'' in ji shi.

BBCHausa

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN