Yan sanda sun yi artabu da ‘yan bindiga, sun dakile yunkurin yin garkuwa da mutane a hanyar Gusau zuwa Sokoto


Rundunar ‘yan sandan jihar Zamfara a ranar Laraba, 21 ga watan Fabrairu ta ce jami’anta sun dakile wani yunkurin yin garkuwa da wasu ‘yan bindiga suka yi a kan hanyar Gusau zuwa Sokoto.


 An tattaro cewa ‘yan bindigar da ke da yawan gaske sun tare hanyar Gusau zuwa Sokoto a kokarinsu na yin garkuwa da masu ababen hawa da ke bin hanyar.


 Majiyoyi a yankin sun bayyana cewa ‘yan bindigar sun yi nasarar yin garkuwa da fasinjoji 26 kafin isowar jami’an tsaro.


 Sai dai kakakin rundunar ‘yan sandan jihar, Yazid Abubakar, wanda ya tabbatar da rufe hanyar ya dage cewa babu wanda aka yi garkuwa da shi.


 A cewar PPRO, ‘yan sandan sun yi nasarar fatattakar ‘yan bindigar tare da dakile yunkurin yin garkuwa da su.


 “Rundunar ‘yan sandan jihar Zamfara na son sanar da manema labarai cewa ‘yan bindiga sun tare hanyar Gusau zuwa Sokoto tare da sace matafiya 26 a kauyen Kwaren Kirya da ke karkashin karamar hukumar Maru ta jihar Zamfara,” inji shi.


 “Amma a ranar 20 ga watan Fabrairun 2024 da misalin karfe 0900 aka samu labari daga Samariyawa nagari cewa ‘yan bindiga sun tare hanyar Gusau zuwa Sokoto da nufin ci gaba da munanan ayyukansu.


 “Da samun labarin, jami’in ‘yan sanda na reshen Maru ya hada tawagarsa da ke yaki da masu garkuwa da mutane tare da hadin gwiwar rundunar ‘yan sandan Mobile Force da aka tura domin su shiga tsakani da hedkwatar rundunar cikin gaggawa, inda suka zage damtse suka yi artabu da ‘yan bindigar.


 “Saboda matsin lambar da gungun ‘yan sandan biyu suka yi musu, ‘yan bindigar sun tsere suka shiga daji da raunukan bindiga.


 “Saboda haka, rundunar ‘yan sandan na son kawar da ra’ayin cewa ‘yan bindigar sun yi awon gaba da fasinjoji 26 a cikin wata motar bas mai dauke da kujeru 18 ta Toyota da wata motar Golf ta Volkswagen, ba labarin gaskiya bane..



 “Babu daya daga cikin matafiyan da aka sace yayin da jami’an ‘yan sanda suka ceto lamarin, an maido da zaman lafiya kamar yadda aka saba, an kuma dauki kwararan matakai don kaucewa sake afkuwar lamarin

.

 Abubakar ya bukaci al’ummar jihar da su ci gaba da baiwa jami’an tsaro bayanan sirri domin taimaka musu wajen kare rayuka da dukiyoyi.


Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN