Dan Arewa Mai Abun Mamaki - Shu'aibu Mungadi

Daga Shu'aibu Mungadi 


An sace maka yara an kai su kudu an canja musu suna da addini, Abin bai dame ka ba 

Wanda bai yi karatu ko na sakandire ba, ya bude chemist a kauyenku har tiyata yake yi, Kana ce masa dafta.

Kabila ne yake maka talla da yaren Hausa, Kuma a saka a gidan radiyon garinku  ba ka ce komai ba.

An yi kasafin kudi an tauye yankin ka, wakilinka a majalisa bai ce komai ba, kaima ba ka ce masa komai ba. 

An kashe maka mutum dari biyu yau ance kuskure ne, ka yi hayaniyar kwana 3, ka koma ka kwanta, gobe an kara kashe 100, jibi 200, gata 300, abin har yabi jikinka ka yi shuru.

An debi rubabbun ministoci an baka kana murna tunda sun fito daga Yan kin ku,

Wakilanku sun samu dama sun dibga sata sun dawo sun  sayi sarauta kana girmama barawo da rawani.

Gwamnan ka ya sace maka biliyan dari, ya maka empowerment na miliyan dari. ka shiga radiyon kana masa godiya.

Ilimin ya tabarbare a yankinku, makaranta primary ta zama wajen kwanan jakai da awakai, amma fa kai Flyover ce matsalarka

Wai dan arewa da yar arewa, wa ya saka maka wannan wawacin?

Daga Shu'aibu Mungadi

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN