Ta faru, ‘Dan wasa zai kai wa Gwamna Abba rikon Yaransa 2 saboda dakatar da shi daga Fim a Kano


Abdul Haseer wanda ya shahara da suna Malam Ali a shirin Kwana casa’in, ya koka game da dakatar da shi da aka yi daga harkar fim. Legit Hausa ya wallafa.


A bidiyon da Abdul Haseer ya fitar a dandalin sada zumunta wanda mu ka ci karo da shi a Twitter, ya aikawa Gwamna Abba Kabir Yusuf sako. 


Jarumin ya sanar da Mai girma Abba Kabir Yusuf cewa an yi masa hukunci wanda a cewarsa, ya saba ka’ida yana kokarin jan hankalin mata. 


Abdul Haseer ya ce burinsa shi ne ganin ya wayar da kan matasa musamman mata, a karshe sai hukumar tace fina-finai ta zarge shi da batsa. 


Jawabin Malam Ali zuwa ga Gwamna Abba


 "Babu wani mahaluki mai hankali wanda zai zo ya ga ‘yarsa, matarsa, kanwarsa ko kuma yayarsa suna rawan zubar da mutunci, suna sa damammun kaya a shafukan sada zumunta, musamman kafa ta Tik Tok. 


Ya Mai girma Gwamnan jihar Kano, wannan dalili ya sa na ke amfani da hanyoyi dabam-dabam wajen ganin cewa na jawo hankalin matasanmu da ni kai na, musamman ‘ya ‘ya mata da yakana, alkunya da kamun kai. 


Ya Mai girma Gwamnan jihar Kano, ina tura sakonnina ba tare da cin mutunci ga addina ko jihar Kano. A matsayinka na uba a jihar Kano, ina so in yi amfani da wannan damar in fada maka cewa an dakatar da ni daga shirya fina-finai a masana’antar Kannywood na shekara biyu ba tare da ka’ida ba." -


 Abdul Saheer 


Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN