Rikici a kasar Saliyo saboda yunkurin juyin mulki yayin da gwamnati ta ayyana dokar hana fita a fadin kasar


An kai hari a safiyar Lahadi kan wani dakin ajiyar makamai na sojoji a Freetown babban birnin kasar Saliyo, a wani yunkurin juyin mulki gwamnatin kasar ta yi zargin an yi, yayin da ta sanya dokar hana fita a fadin kasar nan take.

 Gwamnati ta ce an dakile wadanda suka yi yunkurin kutsawa cikin rumbun ajiyar makamai a wani babban barikin sojoji, amma an bukaci jama’a su zauna a gida.


 Shaidu sun ce sun ji karar harbe-harbe da fashe-fashe a gundumar Wilberforce a birnin, inda aka ajiye makaman yaki kuma mazaunin wasu ofisoshin jakadanci a babban birnin kasar.


 Wasu shaidun gani da ido sun ce sun ji ana musayar wuta a kusa da wani barikin sojin ruwa a gundumar Murray a Freetown.


Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN