Jerin sunayen, hoton alkalai biyar da za su yanke hukunci a kotun sauraron kararrakin zaben shugaban kasa


A ranar Laraba 6 ga watan Satumba ne kotun sauraron kararrakin zaben shugaban kasa za ta yanke hukunci kan karar da jam’iyyun siyasa biyar suka shigar;  PDP, Labour Party (LP), Action Peoples Party (APP), Allied Peoples Movement (APM) da Action Alliance (AA), suna kalubalantar fitowar Bola Tinubu a matsayin wanda ya lashe zaben shugaban kasa a zaben ranar 25 ga Fabrairu, 2023.


 Jaridar The Nation ta ruwaito cewa zaman Panel na mutane biyar na alkalan yana karkashin jagorancin mai shari’a Justice Haruna Tsammani.  

A ranar da za a yanke hukunci, Alkalan biyar za su yi shawara da yuwuwa su kada kuri'a don yanke hukunci na karshe, idan aka samu sabani kan batutuwan da aka gabatar a gaban shari'a.  Hukuncin dai ba shi ne na Æ™arshe ba, saboda wanda bai ji daÉ—insa ba zai iya É—aukaka Æ™ara zuwa Kotun Koli.


 Alkalan da ke jagorantar kotun su ne:

 1. Justice Haruna Tsammani – Babban magatakardar kotun daukaka kara

 2. Justice Stephen Adah – Kotun daukaka kara (Asaba division)

 3. Mai shari’a Monsurat Bolaji-Yusuf – Kotun daukaka kara (Asaba Division)

 4. Justice Moses Ugo – Kano division

 5. Justice Abba Mohammed – Kotun daukaka kara ta Ibadan.

Published by isyaku.com

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN