Jami'an So-Safe Corps, a jihar Ogun sun kaa wani saurayi dan shekara 20 mai suna Ridwan bayan ya kashe mahaifinsa ya cire sassan jikinsa.
$ads={1}
Wata sanarwa daga shugaban rundunar (Dr) Soji Ganzallo ta hannun Kakakin rundunar Moruf Yusuf, ya ce saurayin ya kashe mahaifinsa ranar Alhamis 31 ga watan Agusta da misalin karfe 12 na dare. Ya cite al'aura da hakora hudu daga bakin mahafinsa.
Sai dai saurayin ya tsere bayan aikata laifin kuma daga bisani jami'ai suka kama shi a maboyarsa. Ya gaya wa jami'ai cewa wani Boka mai suna Baba Kekere ne ya bukaci ya kashe mahaifinsa ya kawo wadannan sassa domin yin tsafin samu dukiya.
$ads={1}
Kakain rundunar ya ce saurayin ya ki gaya masu inda za a sami Baba Kekere. An mika saurayin ga jami'an yan sanda don ci gaba da bincike.
Published by isyaku.com